Tuesday, September 18, 2018

Short story: YA YA ZAN YI DA SOYAYYAR KAWAYE?


Na 
Kabiru Yusuf Fagge (Anka)

Ni kaina da abin ya faru a kaina na yi mamaki, amma daga baya sai na sami kaina a wani yanayi na rashin madafa ko fitar da sakamako na hakika, ba mamaki in sami wanda/wadda za ta sama min mafita.

Masoyiyata mai suna Abida Aliyu Barau mun dade da ita kmuna soyayya, tana sona don Allah nima ina sonta don Allah, iyayenmu da 'yan uwa da abokan arziki duk sun san wannan soyayya tamu kuma suna sa mana albarka a ciki, suna taya mu son junanmu, na zama dan gida a gidansu, itama ta zama 'yar gida a wurin iyayena da 'yan uwana. Tana son abin da nake so, nima ina son abin da take so.

Wannan tasa har aka amince min ina fito don aurenta a gidansu. Na fito din, na aika iyayena aka sa rana.

Saura wata daya da kwanaki goma sha uku a lissafe a daura aurenmu, muna zance Abida ta yi bakuwa, mai suna Surayya, wadda kai tsaye wurinmu ta nufo, suka gaisa da Abida, nima muka gaisa, suka dan yi hira kafin ta shiga da ita gida.

Tun zuwan Surayya da muka hada ido da ita na ji wani yanayi a zuciyata, wanda na rinka kokawa da shi, a karshe na tabbatar da mene ne a zuciyar tawa, wato so ne. To, a lokacin na lura, ita ma Surayya ta ji abin da na ji, irin kallon da na yi mata shi ta yi min.

Surayya babbar kawar Abida ce da suka yi karatu tare, sun rabu tsawon shekaru uku da suka wuce, ita ta tafi Misira, sai a wannan satin ta dawo.

Abu kamar wasa, karamar magana ta zama babba, kawai sai soyayya ta kankama tsakanina da Surayya, abin mamaki yadda na ganta ina sonta haka itama take sona. Kar ka yi tunanin cewa akwai wani dalili da ya sa na sota,  sam babu, kawia zuciyata ta ji tana son ta. Domin ba ta fi Abida komai ba, kai in takaita maka labari kyau da fari duk Abida ta fi ta.

Wani babban abin mamaki shi ne da na nutsu sai na ga cewar ban fifita son kowacce a kan kowacce ba a zuciyata, wato yadda nake son Abida haka nake son Surayya (wato 50-50) bambancin daya ne kawai, na riga son Abinda kuma mun fi dadewa da ita.

Wata rana na je gidan su Surayya muna hira, ta ke tambayata "Yanzu kana ganin babu matsala idan Abida ta gane muna soyayya? Ka san ni dai ba zan iya rabuwa da kai ba."

Na yi shiru kafin na ce, "Kar ki damu, zan tuntubeta game da hakan. Kin san dai yadda nake son Abida haka nake sonki." A zahiri kuma haka ne.

Washegari ranar da na je gidan su Abida da maganar, sai da ta yi jim tsawon lokaci kafin hawaye ya fito daga idanunta, ta ce "Kana ganin hakan ya yi daidai Suraj, shin kana ganin ka yi min adalci kenan. Ka san yadda kishi yake a zuci, ka san yadda zuciya take da kissime-kissime..." Ta kasa ci gaba saboda kuka da tasa.

Na ji matuka tausayinta a raina, ji na yi kamaar nima in tayata kukan. A wannan lokacin bamu kara cewa komai ba tsakanin ni da ita, abin yana damuna, ya zame min goma da ashirin.

Ya ya zan yi da wannan hali da na shiga? Kuma ya ya zan yi da soyayyar kawaye biyu aminan juna?

1 comment:

  1. Kaka-kara-kaka. Wannan shine, ' gaba Kura baya Sayaki. '
    Gaskiya ka tafka ganganci

    ReplyDelete

RANAR HAUSA: ƘUNGIYAR HAUSA TA BUK TA CIRI TUTA

 RANAR HAUSA: ƘUNGIYAR HAUSA TA BUK TA CIRI TUTA Nabila Muhammad Ƙungiyar Hausa ta BUK ƙarƙashin jagorancin Kabiru Yusuf Fagge wanda aka fi ...