Sunday, July 12, 2020

WUKAR FAMA na HAJ. HASSANA ABDULLAHI HUNKUYI



TALLA! TALLA!! TALLA!!!
Ina makaranta littafaina? Ina yan sari da masu siyan daddaya? Albishirjnku, WUKAR FAWA zai shiga kasuwa ranar Juma'a 17/7/2020 insha Allahu.DUK MAI SO YA YI MUN MAGANA.
Yammatan Kauyensu kayi ayarin zuwa rafi wanka, daga nan su debo ruwa. A wannan ayari akwai Haire. Sanye take da rigar karen miski mai tsadan gaske, taci kwalliya kamar ba rafi zataje ba, koda yake ance anguwa zasuje da ummanta saita gudu ta biyo kawayenta rafi.
Haire gwanar iya wanka a rafi ne, takan goya yammata biyu a bayanta ta hau kan katon dutse ta sulmiyo cikin rafin sai dai kuji karar ruwa tinjim.
Haire, ta na shirin fadawa ruwa kenan wasu yammatan suka shiga tikar dambe. Kwatsam, saiga Gaje abokiyar hamaiyar Haire ta bayyana da nata zugar kawayen, anan wuri ya sake hargitsewa, yan gaza gani su kayi ta zuga Haire da Gaje har su ka harsala, to amma basu danbace ba.
Wata daga cikin kawayen Gaje ta debo kasa a dukkan hannuwanta, ta zo gaban Haire ta tsaya ta na fadin, "Na lura yau bakya jin yin masifa, kuma Wallahi sai kinyi. Matsoraciya kawai. To inba ga tsoro ba, zabi daya anan. Ga na tsiya gana arziki... "
Bata rufe baki ba, Haire ta kabar da na tsiyar, alamar tsiyar ta ke ji ruwa-ruwa. Ai kuwa take wuri ya koma sansanin danbe. Duk sai yammatan su ka ja tunga suna kallon yadda mata ke ba hammata iska.
Kwatsam! wata wahainiya ta keto ciyayi ta fito. Nan kuma sai kallo ya koma gun wahainiyar, take su ka fara tonon ta, yayinda da take ta rikida kalolin kayansu.
Na karshen kayan da ta rikida, shi ne karan miskin Haire, da haka wahainiyar ta fara sanda zata koma inda ta fito. Kawayen Haire su kayi ta zugata, "Tabdi, wallahi kada ki yarda Haire, wahainiyar nan ta raina ki da yawa, ta rasa kayan wacce zata kwafa ta tafi da shi sai naki? Ba irinki ake takawa a kwana lafiya ba"
Zugar ya sami muhallin zama a zuciyar Haire, don haka a fusace ta sa kafa ta taka wahainiyar...
A Taimaka a taya ni talla!

3 comments:

RANAR HAUSA: ƘUNGIYAR HAUSA TA BUK TA CIRI TUTA

 RANAR HAUSA: ƘUNGIYAR HAUSA TA BUK TA CIRI TUTA Nabila Muhammad Ƙungiyar Hausa ta BUK ƙarƙashin jagorancin Kabiru Yusuf Fagge wanda aka fi ...