Tuesday, July 14, 2020

SAKAMAKON GASAR MARUBUTAN HAUSA TA ALIYU MUHAMMED RESEARCH LIBRARY, GUSAU INSTITUTE (GI), KADUNA




SAKAMAKON GASAR MARUBUTAN HAUSA TA ALIYU MUHAMMED RESEARCH LIBRARY, GUSAU INSTITUTE (GI), KADUNA.


Labaran da suka tsallake zagaye na farko

1. YINI SITTIN DA ƊAYA
2. GUDUNMAWARMU
3. DAMA SUN FADA
4. SANADIYYA
5. DAN WAYE
6. AIKA AIKA
7. KADDARAR ZAWARCI
8. YAN ZAMANI
9. A DALILIN KWARONA VIRUS
10. KA KI NAKA
11. HALIMATU
12. ILLAR ALMAJIRANCI
13. KANA TAKA ALLAH NA TASA
14. BURGAMI A HAMNUN BERAYE
15. WAYE MAKASHINTA

Labaran da suka tsallake zagayen farko
Daga BMB

ALKAWARINMU na HAFSAT SALISU HAMZA





Sunday, July 12, 2020

WUKAR FAMA na HAJ. HASSANA ABDULLAHI HUNKUYI



TALLA! TALLA!! TALLA!!!
Ina makaranta littafaina? Ina yan sari da masu siyan daddaya? Albishirjnku, WUKAR FAWA zai shiga kasuwa ranar Juma'a 17/7/2020 insha Allahu.DUK MAI SO YA YI MUN MAGANA.
Yammatan Kauyensu kayi ayarin zuwa rafi wanka, daga nan su debo ruwa. A wannan ayari akwai Haire. Sanye take da rigar karen miski mai tsadan gaske, taci kwalliya kamar ba rafi zataje ba, koda yake ance anguwa zasuje da ummanta saita gudu ta biyo kawayenta rafi.
Haire gwanar iya wanka a rafi ne, takan goya yammata biyu a bayanta ta hau kan katon dutse ta sulmiyo cikin rafin sai dai kuji karar ruwa tinjim.
Haire, ta na shirin fadawa ruwa kenan wasu yammatan suka shiga tikar dambe. Kwatsam, saiga Gaje abokiyar hamaiyar Haire ta bayyana da nata zugar kawayen, anan wuri ya sake hargitsewa, yan gaza gani su kayi ta zuga Haire da Gaje har su ka harsala, to amma basu danbace ba.
Wata daga cikin kawayen Gaje ta debo kasa a dukkan hannuwanta, ta zo gaban Haire ta tsaya ta na fadin, "Na lura yau bakya jin yin masifa, kuma Wallahi sai kinyi. Matsoraciya kawai. To inba ga tsoro ba, zabi daya anan. Ga na tsiya gana arziki... "
Bata rufe baki ba, Haire ta kabar da na tsiyar, alamar tsiyar ta ke ji ruwa-ruwa. Ai kuwa take wuri ya koma sansanin danbe. Duk sai yammatan su ka ja tunga suna kallon yadda mata ke ba hammata iska.
Kwatsam! wata wahainiya ta keto ciyayi ta fito. Nan kuma sai kallo ya koma gun wahainiyar, take su ka fara tonon ta, yayinda da take ta rikida kalolin kayansu.
Na karshen kayan da ta rikida, shi ne karan miskin Haire, da haka wahainiyar ta fara sanda zata koma inda ta fito. Kawayen Haire su kayi ta zugata, "Tabdi, wallahi kada ki yarda Haire, wahainiyar nan ta raina ki da yawa, ta rasa kayan wacce zata kwafa ta tafi da shi sai naki? Ba irinki ake takawa a kwana lafiya ba"
Zugar ya sami muhallin zama a zuciyar Haire, don haka a fusace ta sa kafa ta taka wahainiyar...
A Taimaka a taya ni talla!

Friday, July 10, 2020

A DALILIN SON KAI - 2 NA IBRAHIM BIRNIWA



A DALILIN SON KAI - 2 NA IBRAHIM BIRNIWA

Zahra’u da Maryam sun keve a cikin xakin Maryam qarfe huxu da rabi ne na yamma a loakcin.Maryam ta xauko album wanda ya kasance cike da hotunan Faruq ta baiwa Zahra’u domin taga gwarzon nata. Zahra’u ta karvi kundin hotunan tariqa buxewa tana kallon kala-kala hotunan Faruq. Kyakkyawan saurayi, ma’abocin iya saka sutura, gaye wayayye ko a hoton. Ta riqa bin hotunan tana kallon su cikin yabawa yayin da suke ‘yar hira ita da Maryam, duk yawancin hirar akan Faruq. A lokacin da ta gama kallon hoton Zahra’u ta tabbatar ya kwanta mata a rai. Ta rufe album xin.

“Mutumin ina ne?” Ta tambayi Maryam.

“Kano.” Maryam ta ce da ita.

“Gaskiya ya haxu, babu shakka kin yi zave. A ina ku ka haxu da shi?”

“A garin nan.” Maryam ta ce, “Ya zo xaurin auren wnai abokinsa, ni kuma ina daga cikin qawayen amarya,sai mukahaxu wajen hada-hadar bikin, ya ji na kwanta masa a rai tun a lokacin da ya fara gani na, saboda hakabai bar garin nan sai da ya bayyanar da soyayyar sa a gare ni, ni kumana amince da shi. Wannan shi ne watan mu kusan na huxu da shi. Mun haxu da shi a watan da muka gama karatu.”

“Gaskiya ya  yi wallahi. Mene ne sana’ar shi?” Zahra’u ta tambaya.

“Fitar da kaya waje, da kuma shigo da na waje ciki.”

Import and export kenan.”

“Sana’ar sa kenan.”

“Ki ce mai kuxi ne gaskiya.”

“Sosai ma kuwa.” Maryam ta ce “In ki ka ga motocin da yake hawa. Xari biyu da hamsin fa ya bani dan shirya wannan bikin.”

“Dubu xari biyu da hamsin?” Zahra’u ta tambaya baki buxe.

“E, wallahi!” Maryam ta tabbatar mata.

Zahra’u ta jijjiga kai, “Lallai ki ce jarumin naki mai gani ne, Allah dai ya tabbatar mana da alkhairi.”

“Ameen.” Maryam ta ce “Na gode da ki kayaba min shi.”

“Na gode da ki ka nuna min shi nima.” Zahra’u ta ce a ranta.

Sun gabatar da duk wani abu da ya kamata su gabatar da dangane da shirye-shirye a ranar koma Maryam ta yi suna tare da Zahra’u tare suka shirya komai. Zahra’u ta fahimci mahaifiyar Maryam, Hanne tana qaunarta kamar yadda mahaifiyarta Umma Hauwa take qaunar Maryam.

Abin da suka yi na qarshe a ranar kafin su dawo gida da magariba shi ne maganar kujeru waxanda za a zazzauna wajen party baiko sun biya kuxi gaba xaya ba rabin kuxi ba. A gajiye suka shigo gidan liqis.

“Sannunku da dawowa.” Hanne ta ce da su.

“Yauwa sannu Umma. Sunka amsa a tare, sannan suke sassamu wuri suka zazzauna a nan tsakar gidan.

“Wash, gaskiya na wujijjiga.” Zahra’u ta ce, “Wai tun ma kafin a zo mai gaba xaya.”

“Ka ji wai ta wujijjiga.” Maryam ta ce, “Sai ka ce ita kaxai ta yi yawon ba da ni ba.”

“To lallai ne ke ki ji yadda na ji.” Zahra’u ta ce “Kin ji ki,ke da kina ta zumuxi ko gajiya ma ba kya ji.”

Hanne da ke can gindin murhu ta yi dariya “Ni ko har da zance ku zo kukarvi girki tun da kun dawo, ni kuma in huta, amma duk kun cika gida da qorafe-qorafe.”

Suka yi dariya.

“Umma ki ka bamu girki ai kuwa a ci jaga-jaga.” Maryam ta ce.

“Ai har gara ma jaga-jaga.” Zahra’u ta ce, sannan ta miqe “Bari dai ki ga na yi wanka ko na dawo garau.” Ta nufi xakin Maryam domin shirin wanka.

“Yi ki fito nima na yi.” Maryam ta ce yayin da ta bi ta a baya zuwa cikin xakin.

Qarfe takwas da rabi na dare.

Zahra’u da Maryam suna kwance akan qatuwar katifar Maryam suna hira, suna jiran barci ya zo ya kwashe su.Ba su fi minti talatin ba da kammala, cin abincin dare suka kwanta saboda a gajiye suke, sakamakon zirga-zirgar da suka yi.

“Zahra’u ina labarin Sani Magaji ne?” Maryam ta tambaya.

“Ke rabu da wannan.” Zahra’u ta ce, “Bai zo ba, wallahi kwata-kwata bai haxu ba.”

“Kai Zahra’u, ke dai kin fiye ruwanido. Ke kenan kullum ki yi ta xauka kina ajiye wa. Ya kamata ki nutsu fa tun kafin kasuwa ta watse.”

“Wa ya gaya miki wancan kasuwar za ta watse?” Zahra’u ta ce, “Ai wannan kasuwar ko yaushe kasa mata kaya ake.”

“Haka ki ke gani?”

“Ya haka na ke gani, haka ne.”

“To shi kenan.” Maryam ta ce, “Yanzu waye gwanin?”

“Ba ni da wani gwani ni.”

“Ke Zahra’u?”

“Wallahi da gaske, duk masu zuwa wuri na, ni ba su yi min ba.” Zahra’u ta ce.

“Ruwan idon ki dai, amma Sanin nan mene ne laifin sa?” Maryam ta ce.

Zahra’u ta xan juya can ta baiwa Maryam baya, “Ina za ki gane laifinsa ke da ba sanin haxuwar maza ki ka yi ba.”

“Ban san haxuwar maza ba kuma na zavo Faruq?” Maryam ta ce.

“Ya zavo ki dai, ba shi ya ganki ya ce yana so ba?” Zahra’u ta ce.

“To dama ni zan je na ce ina son sa ne. Amma kuma da na amince fa?

To ai dolenki neki amince.Wace ce za ta kasa amsa tayin wannan. Gaye ya kai gaye, amma da yake ke mai son kai ce, kina da kamar Faruq, ni kuma ki ke so ki nuna min cewa ba laifi ba ne idan na amincewa Sani, mutumin da ko sutura bai iya sawa ta yi masa kyau ba. Abokin nan nasa Ibrahim ne ma fa yake xan koya masa gayu. Da ma dai Ibrahim xin ne yake so na, to da sai na amince.”

Maryam ta xan yi dariya.

“To ki sace zuciyar Ibrahim xin mana.”

“Tab, wannan ba shi da wata magana kullum sai ta wata wai ita Shafa’atu ‘yar Gusau.”

“Kin tava zuwa Gusau?” Maryam ta tambaya.

“Kai ban tava zuwa ba.”

“Ba ki ma san wajen ina take ba ko?”

“Na sani mana, ba can take ba wajen Baushi?”

“A’a, me ya haxa Gusau kuma da Baushi?” Daga jihar Sokkwato fa aka cire ta.”

“Haba?”

“Allah.”

Haka suka yi ta hira har barci ya xauke Maryam. Zahra’u ba ta sani ba tana ta magana sai ta ankara Maryam ba ta amsawa.

“Maryam!” Ta kira sunanta.

Shiru, ta tabbatar Maryam ta yi barci, sai ta yi shiru itama, ta lumshe idanuwanta ta faxa kogin tunani. Tunanin faruq, mutumin da ba ta tava ganin sa a zahiri ba sai a hoto. Zuciyarta ta karkata gaba xay zuwa gare shi. Ta matsu Talata ta yi domin ya zo ta ganshi a zahiri. Kwanaki ukun da suka rage Talata ta zo sai take ganin su kamar wasu sati uku. Abin da yake tava ranta shi ne sanin cewa babu yadda za ayi ta ganshi dole sai ranar Talatar nan idan ya zo.

Ta tashi zaune a hankali, sannan ta miqa hannu kan wani xan tebur da ke gefen katifar, da suke kwance ta xauko album xin da ke xauke da hotunan Faruqu. Ta buxe album xin ta  riqa kallon hotunan xaya bayan xaya. A lokacin data gama kallon hotunan sai ta album xin ta rungume a qirjinta, tana mai ina ma ina ma, ina ma da ita suka haxu ba da Maryam ba, ina ma ita yake so ba Maryam ba, ina ma baikonta za a yi gata ba na Maryam ba.

Ta xan juya ta dubi Maryam dake kwance tana barci abin ta.

Barcin  ta ma take saboda babu abin da ya dameta ta mallaki saurayi da ya kwanta min a rai. Ta xan jima tana dubanta. Sannan sai ta xaukie kai ga barin kallonta, sannan ta juya ta maida album xin ta ajiye a wurin da ta xauka.

Ta miqa hannu ta kamo makunnar lantarki ta gado ta kashe wuta, duhu ya gauraye xakin, sannan ta rufe idanuwanta ta gayyato barci. Barcin bai zo ba sai bayan da ta shafe sama da minti goma sha biyar tana tunanin Faruq.

Can cikin dare a cikin barcin ta sai ta yi mafarki ana biki. Kuma tana xaya daga cikin qawayen amarya, sai abokan ango suka zo maganar kuxin zanchen, sai ta ga har da Faruq a cikin su. Ya kura mata idoyana ta kallon ta ita ma tana ta kallonsa. Can sai ya kira ta suka keve su biyu.

‘Ina son ki.’ Ya ce da ita.

‘Ina son ka nima.’ Ta amsa masa.

Sai ta ga ya qyalqyale da dariya. Yana ta dariya sai ta ga ya juye ya koma Sani. Ashe dama ba Faruq ba ne Sani ne. Sani ya juya baya yana ta dariyar jin daxin ta ce tana sonsa.

Sai taji ranta ya vaci ‘Bana son ka, ba na sonka...ba na sonka.’ Ta riqa faxa cikin tsawa.

Sani ya juyo. Yana juyowa sai ta ga Faruq ne, ya daina dariya ya vata rai.

‘Ba kya sona?’ ya ce da ita ‘Shi kenan na gode.’ Ya juya, ya tafi, ya bar ta.

A xan lokacin sai ta ruxe ta rasa yadda za ta yi, sai kuma ta daidaita qwaqwalwarta.

‘Ina sonka....ina son ka....’ ta faxa da qarfi. Ta tabbatar ya ji, amma kuma bai tsaya ba ya ci gaba da tafiyar sa, sai ta bi shi da gudu tana ta faxin ‘Ina son ka....’ina son ka...’ tana gudun sai ta yi tuntube ta faxi. Ta yunkura za ta tashi, sai ta farka daga barcin da take.

Da farko ta xan yi jim anan a kwance, tana qoqarin rarrabewa tsakanin mafarkin da kuma gaske. Ta ja dogon numfashi  bayan da ta fita a mafarki, shiru babu wuta an xauke. Ta ji haushi saboda tana son ta sake kallon hoton Faruq. Duk da haka sai ta juya ta sa hannu amma sai ta bubbuxe album xin, ba ta ganin komai xin kuwa sai duhu, ta rufe album xin  ta rungume shi a qirjinta ta faxa tunanin Faruq.

Rungume da hoton a qirjinta, barci ya sake xauketa.

Qarfe takwas na safe maryam ta farka daga barci, da yake xakin a kulle yake har yanzu hasken qwan lantarki yana da tasiri a xakin. Zahara’u ba ta kashe wuta ba kenan, maryam ta zata. Ta tashi, ta zauna nan akan katifar yayin da ta yaye mayafin da take lulluve dashi. A hankali ta juya, ta dubi Zahara’u dake kwance a gefenta tana barci, ga mafarkinta sai ta ga Zahara’u tana rungume da album xin dake xauke da hotunan Faruq. Ta xan jima tana kallon Zahara’u, a cikin zuciyarta tana jujjuya abin da ta gani, tan son ta fahimci al’amarin irin fahimtar da ya dace mene ne hakan ke nufi? Me ya kai Zahara’u rumgume hotunan Faruq har tayi barci da su a qirjin ta.

Maryam tayi tunanin abubuwa da dama amma ta kasa tsaida tunanin ta a kan wani abu guda xaya. Abin da zuciyarta ke qoqarin saqa mata ba za ta amince da shi ba, ba za ta yarda yadda suke da Zahara’u wani abu makamancin abin da zuciyarta take karkata gare shi zai kasance ba.

Ta sa hannu a hankali ta zare album xin daga qirjin Zahara’u ta ajiye shi a wurin da ta saba ajiyewa, sannan sai ta xan doki kafaxar Zahara’u, ta sake  duka. Zahara’u ta farka a hankali, ta buxe idanuwanta kaxan tana xan yatsina fuska a qoqarinta na baiwa idanuwanta damar karvar hasken da ke gauraye da xakin.

Bayan idanuwanta sun tabbatar da sun amince da hasken sai ta buxe idanuwan natasosai ta dubi Maryam dake zaune a kan katifar a gefenta kana tayi miqa da hamma tare da yin salati.

“Tashi gari ya waye.” Maryam ta ce da ita.

Misalin karfe tara da rabi sun kammala da komai. Maryam ta shigo musu da kayan karin kumallo xaki, suka zauna suna ci suna kuma hirar abubuwan da suka shafe su da ma waxanda ba su shafe su ba kamar yadda qawaye suka saba yi. Can cikin hira bayan Maryam ta yi shawara da zuciyar ta sai ta amince ya kamata ta tuntuvi Zahara’u game da al’amarin da ya fara yi mata barka da asuba bayan ta shin ta daga barci yau.

“Zahara’u zan yi miki tambaya.” Maryam ta ce da Zahara’u.

“Ina sauraronki.” Zahara’u ta ce da ita.

Maryam ta kurvi shayi daga kofin da ke riqe a hannunta ta haxiye, sannan ta dubi Zahara’u.

“Wane matsayi ki ka baiwa Faruq nawa a wajenki?”

“Matsayi?”  Zahara’u ta ce “Wane matsayi kuwa ban da matsayin da ya dace da shi?” Zahara’u ta amsa mata.

“Kamar wane matsayi kenan ki ke zaton ya dace da shi?”Maryam ta tambaya.

“Saurayin qawata mana.” Zahara’u ta ce “Yana da wani matsayi da ya wuce ne? Me ya sa ki ka yi min wannan tambayar?” Ta xauki kofin shayi, ta nufi bakinta da shi.

“Na farka daga barci ne yau sai na gan ki rungume da album xin hotunan Faruq, shi ne nake son na san dalilin faruwar hakan.”

Zahara’u ta fasa kurvar shayin da ta kai bakinta, ta dawo da kofin qasa ta ajiye, zuciyarta na jujjuya abin da Maryam ta faxa cikin gaggawa tana son ta tuna abin da ya faru daren jiya da kuma amsar da ta fi dacewa ta baiwa Maryam.

Yanzu jiya barci ta yi album a qirjinta. Ya aka yi ta fara bada qofar da Maryam za ta fahimci wani abu tun yanzu. Ta dubi Maryam za ta fahimci wani abu tun yanzu. Ta dubi Maryam ta yi ‘yar dariyar qarfin hali.

‘Me ki ke so ki ce?’

‘Me na me ke so na ce, ko kuma me na ke so na ji?’ Maryam ta ce.

‘Kar fa ki yi wani tunani na shirme.’ Zahara’u ta ce.

‘Ba zan yi ba.’ Maryam ta ce ‘Shi ya sa ai na tambaye ki.’

‘Ok. Jiya na yi barci, can sai na yi wani mafarki mai ban tsoro, sai na farka nan da nan ke kuwa a lokacin kina barcin ki. Bayan wannan farkawar sai kuma barci ya qi wuza min. Na kwanta nan kawai idona buxe, cike da gundura. Na jima a haka barci bai zo ba, sai na kuma wuta na xan duba ko zan sami wani littafin karatu amma ban ga komai ba, shi ne sai na xauki album xin ina dubawa, ina gayyatar barci. Ban san lokacin da yayi awon gaba dani ba.

 “Ke da me ki ke zato?”

“Babu komai.” Maryam ta ce, sannan ta kurvi shayi ta ajiye kofi, “Kin san ina ji da shi, ina matuqar qaunar sa, ina kuma matuqar kishin sa.”

“Kina kuma matuqar zargi a kansa.” Zahra’u ta ce.

“Idan haka ne za ki ga laifi na?” Maryam ta tambaye ta, tana kallonta cikin ido.

“Ba zan ga laifin ki ba.” Zahra’u ta ce, “Ba zan ga laifin duk wata qawa da ta zargi qawarta da son saurayinta ba.”

“Za ki ga laifin ita qawar da aka zarga idan ta yi fushi?” Maryam ta tambaye ta.

“In dai tabbas an zarge ta xin.” Zahra’u ta ce. Sannan ta shi tsam daga gaban kayan karin kumallon ta koma bakin katifa ta zauna, sannan ta kwanta da baya akan katifar, yayin da qafafunta ke qasa. Ta yi qoqarin nuna fushi a fuskarta. Ya kamata ta nuna ranta ya vaci don hakan ya raunana zargin da Maryam take a ranta.

Maryam ta bi ta da kallo har ta kwanta xin, sannan ta ja dogon numfashi. Ba ta kyauta ba, ya za ta zargi qawarta qud da qud da son saurayin ta, bayan kuma ta faxi dalilin da ya sa ta same ta rungume da album xin hotunan saurayin nata.

“Ki yi haquri Zahra’u.” Maryam ta ce cikin sanyin rai, “Kin san yadda zuciya take kuma kin san yadda so ya ke. Bai kamata na zargi wani abu ba na sani amma na kasa hana kaina ne ki yi haquri don Allah, na gamsu da bayanin ki.” Ta yi shiru don jin abin da Zahra’u za ta ce, amma shiru ba ta ce komai ba.

“Zahara’u!” Ta kira sunanta.

“Don Allah ki qyale ni.” Zahra’u ta ce.

“Ki yi haquri don Allah don Annabi, I am sorry.”

 “Haba Maryam.” Zahra’u ta ce, “Ya ma za a yi ki yi min haka? Don kawai ke kina son Faruq sai ki xauka kowa ta ganshi za ta so shi, har ki fita a hankalinki ki zarge ni da sonsa, an ce miki Faruq ya yi min ne. Na fa yaba shi don kina sonsa, bai kamata na kushe miki shi ba...”

“Na dai ce ki yi haquri don Allah... Haba Zahra’u, ya wuce don Allah, Allah ya huci zuciyarki.”

Matsala.” Zahra’u ta ce a ranta, “Akwai babbar matsala.”


Monday, July 6, 2020

GASAR RUBUTATTUN GAJERUN LABARAN HAUSA TA ARCH. AHMAD MUSA DANGIWA




GASAR RUBUTU! GASAR RUBUTU!!
SANARWA! SANARWA!! SANARWA!!!

GASAR RUBUTATTUN GAJERUN LABARAN HAUSA TA
ARC. AHMAD MUSA DANGIWA
BISA MANUFOFIN BABBAN BANKIN BADA LAMUNI DON MALLAKAR GIDAJE NA ƘASA. (FEDERAL MORTGAGE BANK OF NIGERIA)

Wannan gasa wata dama ce da za ta taimaka wajen bunkasa rubutaccen adabin Hausa da ya danganci gajerun labaran zube na Hausa, a karkashin jagorancin Arc. Ahmad Dangiwa, bisa manufofin babban bankin bayar da lamuni don gina gidaje na Kasa.

MAUDU'IN GASA
Maudu'in gasar zai kasance wani linzami da ake da yakinin cewa za ya ja akalar tunanin marubuta domin su fito da batutuwan;
• Tasirin da ke tattare da mallakar muhalli, da kuma wasu illoli da ka iya shafar rashin mallakar muhallin.
• Matsalolin da ake fuskanta na tsara muhalli ba bisa ka'ida ba, da suka hada da shata filaye ba bisa ƙa’ida ba, tare da gina muhalli a wuraren da ba su dace ba, kamar rashin gina magudanan ruwa, da illar da hakan ka iya haifarwa a cikin al’umma musamman ta fuskar kiwon lafiya da tsabtace muhalli.
• Fito da matsalolin da gine-gine marasa inganci ka iya haddasawa, da suka hada da asarori masu dimbin yawa, na dukiyoyi da rayuka da ma rasa muhallin kacokam!
Tilas masu gasa su yi anfani da salon ayyanawa na gajerun labaran zube na Hausa.

ABUBUWAN DA AKE SA RAN GASAR ZATA SAMAR BAYAN KAMMALA TA
• Samar da littafin zube Sukutum wanda ke ɗauke da labarai da suka danganci muhalli a cikin Harshen Hausa
• Fito da ayyukan bankin bayar da lamuni don samar da gidaje na ƙasa ƙarkashin jagorancin Arc. Ahmad Musa Ɗangiwa cikin sigar labaran zube.
• Fito da Fasihan matasa marubuta waɗanda ke da wata baiwa ta musamman da su kan iya tsayuwa akan ta domin dogaro da kai, musamman ta sigar yadda ake zana taswirar gida da tsara muhalli a cikin zube.
• Fito da girman matsalolin da ke akwai a ɓangaren muhalli tare da wayar da kan al’umma kan muhimmancin mallaka da kuma kiyaye muhalli.
• Jawo hankalin ‘yan kasuwa da kamfanoni da su zuba jari a fannin samar da muhalli
• Jawo da hankalin gwamanti da hukumomi wajen sa ido game da yadda ake samar da muhalli tare da bin doka wajen shata filaye na tsarin garuruwa da unguwanni.

TASWIRAR GASA
An ba da dama ga marubutan Hausa, maza da mata, su aiko da samfurin labarin da za su rubuta mai ɗauke da kalmomi 1000. A tabbata an turo da samfurin kai tsaye ga dangiwaliterary2020@gmail.com zuwa ranar 04 ga watan Agusta, 2020. Za a tace da zabar 20 daga cikin samfurin labaran da aka aiko waɗanda suka fi burgewa a watan Augusta, 2020 Daga nan za a nemi masu waɗannan samfuran labaran guda 20 da su halarci wata bita ta musamman ta kwana 1 da za a yi a birnin Katsina a watan Satumba, 2020, don koya musu abin da ake buƙata da yadda za su tsara labaran domin su dace da manufar da aka assasa gasar inda daga karshe, za a zabi labarai goma da suka yi zarra domin fitar da na daya zuwa na goma.
Ana sa ran waɗanda suka halarci bitar su koma gida su kammala rubutun labaran zuwa watan Octoba 2020. Za a ba da awalaja ga mutane ashirin da labaran su suka samu zuwa zagaye na gaba (waɗanda suka halarci bitar).
Za a tace da tsara da kuma buga labaran, a ƙaddamar da su a wani gaggarumin biki da za a shirya a Katsina, a watan Disamba da yardar Allah.

DOKOKIN RUBUTUN
Domin shiga wannan tsarin samar da gajerun labarai na Hausa wanda zai kasance mai ɗauke da kalmomi 5000, marubuta na da damar su yi bincike da nazari da tuntuɓa na tsawon wata ɗaya kafin aiko da labaran, bayan halartar bita da aka shirya musu.
1. Ba a kuma buƙatar sai ana da wani kwali ko satifket na musamman kafin a kasance cikin wannan tsarin samar da labarai, illa iyaka gwaninta da fasahar tsara labaran Hausa. Ana kuma bukatar rubutun ya dace da batutuwan da suka shafi muhalli da fasahar zane-zanen gidaje da ayyukan bankin bada lamunin gina gidaje na ƙasa ƙarƙashin jagorancin Arc. Ahmad Musa Ɗangiwa ke gudanarwa da sauran makamntansu.
2. Dole ne ya kasance an yi amfani da ka'idojin rubutu bisa daidaitaciyar Hausa.
3. Dole ne a yi rubutun bisa tsarin haruffa masu ƙugiya, kuma rubutun ya kasance an aika shi bisa tsarin Microsoft word ko PDF. Zuwa ga wannan email din dangiwaliterary2020@gmail.com
4. Wajibi ne labaran su kasance sabbi waɗanada ba a taba shiga wata gasa da su ba ko kuma buga su a wasu jaridu ko zauruka na kafafen sadarwa.
5. Wannan gasa ba ta buƙatar ayi haɗin guiwa wajen shigarta ana buƙatar daidaikun mutane ne kawai mace ko namiji.
6. Wannan gasar buɗe take ga duk wanda ya iya rubutu da harshen Hausa ne kadai,matuƙar da zai iya kiyaye dokoki da ƙa'idojin da aka gindaya.
7. Wajibi ne a aiko da somun taɓi na kalma dubu (1000) daga 12 dare na ranar 4 ga watan Yulin 2020 zuwa 17 na hudu ga watan Agustan 2020.
8. Duk labarin da aka shiga gasar da shi mallakin gasa ne, ba a yarda a sake ɗaukar shi a shigar da shi wata gasa ba ko makamancin haka.
9. Hukuncin da alkalan gasa suka yanke shi ne na ƙarshe ba za a sake tattaunawa ko duba hukuncin ba, bayan fitar sakamako.
10. Wajibi ne duk wanda zai turo da labarinsa ya aiko da lambar wayarsa da takaitaccen bayani game da shi.

KYAUTUKAN DA ZA A BAYAR
Za a bada kyautuka ga waɗanda suka shiga gasar daga na daya zuwa na goma kuma a buga littafin, a kaddamar da shi a yayin bikin bayar da kyautukan. Ga yadda tsarin kyaututukan zasu kasance.
a. Kyautukan da za a bayar ga mutane uku na farko
i. N250,000 ga wanda ya zo na ɗaya
ii. N150,000 ga wanda ya zo na biyu
iii. N100,000 ga wanda ya zo na uku
iv. Wanɗanda suka zo na huɗu zuwa na goma kowanensu za a bashi kyautar N50,000
Za a bayar da Kambu ga na daya zuwa na uku, sannan kuma dukkan mutane goma da suka yi zarra za a basu takardar sheda wadda take ɗauke da sa hannun shugaban hukumar bankin bayar da lamuni don gina gidaje na kasa Arc. Ahmad Musa Ɗangiwa.
Domin tuntuba ko ƙarin bayani
08036954354
09022709603

Wednesday, July 1, 2020

SHARHIN LITTAFIN RUBUTUN FIM na BALA ANAS BABINLATA



SHARHI A KAN RUBUTUN FIM, NA BALA ANAS BABINLATA

Daga

Yusuf M. Adamu PhD, MNAL

Sashen Labarin Qasa, Jami’ar Bayero, Kano

 

Monday, June 29, 2020

MUJALLAR "INUWAR MARUBUTA" (don cigaban marubuta)



INUWAR MARUBUTA (don cigaban marubuta)

(Fitowa Ta 2, Fabarairu 2005)

Tuna baya: Labarun shekaru 15 baya

Kudinta N50

LABARUN DA SUKE CIKI

-MARUBUTA ZA SU DAIDAITA SAHU?

Taron marubuta da hukumar A Daidaita Sahu, domin daidaita sahun fannin rubuce-rubuce

-BAN GOYI BAYAN RUBUTUN BATSA BA...- ZAINAB LAWAN BIRGET

Hira da marubuciya, Zainab Lawan Birget, inda ta nuna rashin goyon bayanta ga rubutun batsa.

 

A DALILIN SON KAI -1



` A DALILIN SON KAI

(LABARIN ZAHARA’U)

 

Daga

 

IBRAHIM BIRNIWA

birniwaalmout@yahoo.com


BABI NA XAYA

Zahara’u ta daxe tana jin ana cewa Haxejiya Ginsau Birnin Doki, amma bata tava zuwa. Haxejiya ba sai yau tun da ta sauka a mota take ta waige-waige don ta tabbatar da Haxejiya ta dace da yadda take jin labarinta a bakin mutane musamman qawarta Maryam da ta zo bikin baikonta a yau wannan rana ta Asabar.

Haxejiya ba ta yi qasa a gwiwa ba wajen gamsar da zuciyar Zahara’u cewa ta isa a bada labarin ta a ko’ina.

HAJIJIYA na IBRAHIM BIRNIWA


Friday, June 26, 2020

BAKAR ANIYA




BAKAR ANIYA
Na Aminu Ladan Abubakar (Ala)
2002
(tsohuwar taskar)

Kakkarfar iska mai sanyi ta cigaba da kadawa hade da kugin ruwa da ke gudana ta karkashin gadar, karfin kadawar iskar dake kokarin fisgar mayafin dake jikinta, shi ya bai wa doguwar rigar dake jikinta damar kadawa tamkar tuta.

Wadansu zafafan hawaye, suka cigaba da sintiri wasu na bin wasu suna disa bisa jaririn dake tallabe a hannunta. wanda lokaci zuwa lokaci cikin wutsilniya yakan canyara kuka a lokaci guda kuma sai ka ga ya sanya hannunsa a baki yana tsotsa.

Wani lokaci kuma a garin wautsilniyarsa har yakan yakushi fuskarsa da faratansa a lokacin ne to za ka ji sautin kukansa ya yi amsa kuwwa a sararin wannan bigire da ake kokarin yi masa muhalli a gurin.

A lokacin da ta doshi karkashin gadar zuciyarta ta yi bakikkirin ta duhunta ganinta, kugi da ambaliyar da ruwan ya rika yi, yana marin juna, shi ya haifar da juwa a tare da ita sai ta rinka jin tamkar fizgarta ake yi izuwa cikin wannan ruwa. Sannu a hankali tana bin gefen ruwan ba ta ankara ba kafarta ta zame...
-Aminu Ala

Wednesday, June 24, 2020

SIYAMA na Yakub M. Kumo




SIYAMA
Sirrin afkawar al'amuransa cikin laulayi ya samo asali ne, sakamakon zazzafan zazzabin soyayya mai tsannain karfi da ya sarkafe zuciyarsa. Ko da tarin hannu-da-shuni da ya mallaka ba su zama katangar shiga tsakaninsa da Siyasama ba shu'umar matarsa mai matukar girman kai da ta dauki duniya a matsayin gidan-kashe-ahu, ba za ta taba barin macen da ba ta iya daurin kallabi ta zama kishiya gareta ba.

Shakka ta lullube zuciyarsa yayin da ya yi zaman farko da mahaifinta wanda miskilancinsa ya fifita a kan na mislika, duk da hakuri, juriya da kuma kasancewar sa ma'abocin riko da sunnah kamar Maimunatu sai da ya yi masa jagora ga hajijiya.
Zaman gida ya gagare shi, ya kuma gabatar da abubuwan al'ajab, amma duk da haka iya ruwansa bai kai shi ga kubuta ga siradin da ke gabansa ba.
Dankari, daga karshe ministan gidajen da ayyuka ya shiga rudanin da ya jefa duniyarsa ga hatsabibiyar rayuwa.
Sharhi daga Maje ElHajeej Hotoro
Siyama na Yakub Moddibo Kumo

Alƙalancin Gasar Rubutu

 Alƙalancin Gasar Rubutu Bayan da na saurari bayanan wasu alƙalan gasannin rubuce-rubucen ƙagaggun labarai a mabambantan gasanni, na tsinkay...