Thursday, January 23, 2020

LITTAFIN KOYAR DA TAJWEEDING RIWATY QALUN




Wannan littafi mai suna TAJWEEDIN RIWAYATI QALUN fassara ne na littafin (SHARHI RISALATI QALUN) wanda Shehin Malami Aliyu Muhamad Ad-Dhiba’i mutumin Misra ya rubuta, shi ma kuma sharhi ne ya yi a kan baitocin da Shehin Malami Muhammad Sa’udi ya tsara a bisa hukunce-hukuncen tajweed da Imamu Abu Musa Isah, wanda aka yi wa laqabi da Qalun, wanda shi Shehu ALiyud Dhiba’i ya yi sharhin sa da Larabci, shi kuma Malam Muhammadus-Su’udiy ya tsamo hukunce-hukunce ne daga littafin Shaxibiy.

Kamar yadda daga kowa ya sani ne, riwayar Warshe da Hafsu sun rigaya sun bazu ko ina a birni da qauye a qasar nan, savanin riwayati Qalun wanda ba kowa bane ma ya san da ita ba, don haka nag a ya dace a bisa xan abin da Allah yah ore min in fassara littafin (SHARHI RISALATI QALUN) da harshen Hausa tare da yin bayani dalla-dalla da fitar da hukunce-hukuncen da aka qudundune a ciki a fili don burin samun ci gaba da qaruwa a cikin tajweedin Al-Qur’ani tare da bunqasa karatun Al-Qur’ani a qasar nan.
Babu shakka babba da yaro, namiji da mace za su fa’idantu da wannan littafi. Ina fatan Allah ya sa albarka a cikinsa, Allah ya ba shi karvuwa kuma ya albarikaci qasar nan da makarantun Al-Qur’ani da riwayati Qalun da sanadinsa wannan littafi nawa kamar yadda ya azurta qasar nan da makaranta AL-Qur’ani da riwayati Hafsu da Warshu.
Na gode,
‘YAR’UWARKU

NAFISATU YUSUF ABDULLAHI BICHI
MRS. DAYYIB SHEIKH DAN-ALMAJIRI
RIJIYAR LEMO, LAYIN XAIBA
KANO STATE

No comments:

Post a Comment

RANAR HAUSA: ƘUNGIYAR HAUSA TA BUK TA CIRI TUTA

 RANAR HAUSA: ƘUNGIYAR HAUSA TA BUK TA CIRI TUTA Nabila Muhammad Ƙungiyar Hausa ta BUK ƙarƙashin jagorancin Kabiru Yusuf Fagge wanda aka fi ...