Thursday, January 23, 2020

LITTAFIN KOYAR DA TAJWEEDING RIWATY QALUN




Wannan littafi mai suna TAJWEEDIN RIWAYATI QALUN fassara ne na littafin (SHARHI RISALATI QALUN) wanda Shehin Malami Aliyu Muhamad Ad-Dhiba’i mutumin Misra ya rubuta, shi ma kuma sharhi ne ya yi a kan baitocin da Shehin Malami Muhammad Sa’udi ya tsara a bisa hukunce-hukuncen tajweed da Imamu Abu Musa Isah, wanda aka yi wa laqabi da Qalun, wanda shi Shehu ALiyud Dhiba’i ya yi sharhin sa da Larabci, shi kuma Malam Muhammadus-Su’udiy ya tsamo hukunce-hukunce ne daga littafin Shaxibiy.

Kamar yadda daga kowa ya sani ne, riwayar Warshe da Hafsu sun rigaya sun bazu ko ina a birni da qauye a qasar nan, savanin riwayati Qalun wanda ba kowa bane ma ya san da ita ba, don haka nag a ya dace a bisa xan abin da Allah yah ore min in fassara littafin (SHARHI RISALATI QALUN) da harshen Hausa tare da yin bayani dalla-dalla da fitar da hukunce-hukuncen da aka qudundune a ciki a fili don burin samun ci gaba da qaruwa a cikin tajweedin Al-Qur’ani tare da bunqasa karatun Al-Qur’ani a qasar nan.
Babu shakka babba da yaro, namiji da mace za su fa’idantu da wannan littafi. Ina fatan Allah ya sa albarka a cikinsa, Allah ya ba shi karvuwa kuma ya albarikaci qasar nan da makarantun Al-Qur’ani da riwayati Qalun da sanadinsa wannan littafi nawa kamar yadda ya azurta qasar nan da makaranta AL-Qur’ani da riwayati Hafsu da Warshu.
Na gode,
‘YAR’UWARKU

NAFISATU YUSUF ABDULLAHI BICHI
MRS. DAYYIB SHEIKH DAN-ALMAJIRI
RIJIYAR LEMO, LAYIN XAIBA
KANO STATE

No comments:

Post a Comment

MAKAHO MAI FITILA

MAKAHO MAI FITILA Wani saurayi yana yawo da dare sai ya hangi wani mutum da fitila. Da suka gamu, ya ga ashe makaho ne. Ya ce, "Kai wa...