Tuesday, October 9, 2018

Short story: ADDU'AR MATA


ADDU'AR MATA

Kabiru Yusuf Fagge (anka)



Hannayena a sama, fuskata na fuskantar Ka'aba ba kiftawa, na zurfafa sosai a wajen yiwa kasata addu'a, fatana Allah ya shiryi al'ummar cikinta tun daga talakawa, masu hannu da shuni zuwa shugabanni.

A zahiri wani dan siyasar gundumarmu ne ya biya min kudin Umra don in zo in yi masa addu'a ya sami fada a wajen gwamna da shugaban kasa, sannan in yi masa addu'a Allah ya sa ya kara lashe zabe mai zuwa.

Ni kuma a zahiri tun lokacin da zai biya min, na so ya ba ni kudin na kara jari sannan na taimaki makobta, amma na lura ba zai yi haka ba, idan ma na ce hakan to zan iya yin biyu-babu. Don haka na hakura, aka biya min muka taho.

Da na zo kasa mai tsarki na lura ba abin da ya fi muhimmanci da ya wuce in yiwa kasata Nijeriya addu'ar Allah ya kintsata ya daidaita lamuran mutanen cikinta, don kowa ya sani ana cikin matsala.

*

A yayin da na fara yin kasa-kasa da addu'ar, sai na jiyo wata mata Bahaushiya da ke gefena tana yin tata addu'ar wadda ta ja hankalina, cewa take:

"Allah don kadaitar zatinka da kyawawan sunayenka, Allah don isar mulkinka, Allah ka sa mijina ya talauce, Allah ka sa kafin na koma gida Nijeriya mijina ya zama fakiri."

Haka take ta maimaitawa, dole ba shiri na tsaya da duk abin da nake yi, na koma gefe ina kallon matar nan, har ta gama, ta taso za ta wuce ni. Na yi sauri na tare ta.

"Baiwar Allah in tambayeki mana."

Ta kalle ni a dake, "Ba sai ka tambayeni ba, ka ji ina addu'a ko?"

Na gyada kai, "Addu'a mai ban mamaki kuwa."

Ta yi murmushi a baibai, "A wajenka ce mai ban mamaki, amma mu a wajenmu mata wannan addu'a ce mai kyau. Kwanan nan mijina ya yi kudi kuma shi ya biya min wannan Umrar da na zo, na ga take-takensa ne daga yin kudin nan yana so ya kara aure shi ya sa nake masa addu'ar ya koma gidan jiya, ka ga idan yana fakiri ba zai iya kara aure ba."

"Amma kina da abin mamaki baiwar Allah..." Na ce da ita.

Ta katse ni "Nawa mai sauki ne Malam, da yawa matan da suke gida suna yiwa mazajensu addu'ar kada su yi kudi. Masu sukunin kuma matansu suna yi musu addu'ar Allah ya sa su talauce don kar su yi musu kishiya. Akwai wata tambayar?"

Na gyada kai na ce "Babu, sai dai in ce Allah ya kyauta."

"Amin." Ta ce, ta wuce.

No comments:

Post a Comment

RANAR HAUSA: ƘUNGIYAR HAUSA TA BUK TA CIRI TUTA

 RANAR HAUSA: ƘUNGIYAR HAUSA TA BUK TA CIRI TUTA Nabila Muhammad Ƙungiyar Hausa ta BUK ƙarƙashin jagorancin Kabiru Yusuf Fagge wanda aka fi ...