RAMAKON ALHERI...
Gajeren Labari
Kabiru Yusuf Fagge
Wani Alhaji ne, yana da shago a kasuwar Sabongari, yana
sayar da kayan 'karau, sai wani bawan Allah ya zo gare shi, ya roke shi, ya ba
shi gefen shagon nasa don ya rinka sayar da kayan miya, idan ya so ko wani abu
sai ya rinka biya a matsayin kudin haya.
Alhajin nan ya ce ba komai, ya zauna ba sai ya rinka bayar
da komai ba, Malam mai kayan miya, ya yi godiya, washegari ya fara sana'arsa ta
sayar da kayan miya.
Yau da gobe, Allah ya buda wa mai kayan miya, ya habaka,
yana ciniki sosai. To zuciya ba ta da kashi, da Alhaji mai kayan karau ya ga
haka, sai zuciyarsa ta rinka kulla masa mugun abu, don haka watarana sai ya
kira Malam mai kayan miya, kai tsaye ya ce masa lallai yana so ya tashi daga
gefen shagonsa yana son wurin.
Malam mai kayan miya ya yi ta rokonsa Allah - Annabi ya yi
masa hakuri, ya kyale shi ya ci gaba da kasuwancinsa, amma fafur Alhaji mai
kayan karau ya ki, ya ce, ya ba shi zuwa jibi ya tashi.
Haka, Malam mai kayan miya yana hawaye, yana komai, ya bar
wurin. Bayan tafiyarsa, Alhaji ya dubi abokinsa ya ce, "Ai ni ma, wani zan
kawo in rinka saro masa kayan miyar yana siyar min, ina biyan shi."






