Tuesday, May 12, 2020

ABOKIN DARIYA: Hausa Novel



Abokin
DARIYA



Na





 


              
KABIRU YUSUF FAGGE (anka)
07030319787


Haqqin mallakar littafi (m) Kabir Yusuf Fagge Anka
 
Copyrights (c) Kabir Yusuf Fagge Anka
 
An fara bugawa a 2016
 
Bugawa da yaxawa
GIMBIYA PUBLISHERS FAGGE
Layin Kasuwar Mata, Fagge D2, Kano.
 
Bugawa a na'ura:
Anka-Graphics Fagge
709 G/Lemo, Fagge D2, Kano.
07030319787




YARO MAI SURUTU
W
ani yaro ne sarkin surutu ya tambayi mahaifiyarsa ya ce “Momy wai me ya sa wasu wurare a gashin kanki ya koma fari?”
Mahaifiyar yaron nan ta yi shiru tana tunani, can wata hikima ta faxo mata, ta yi tunanin bari ta yi amfani da wannan damar wajen koyawa yaron darasin rayuwa, sai ta ce “Saboda kai ne hakan ke faruwa xana. Wato duk lokacin da ka yi wani abu mara kyau sai gashina xaya ya zama fari.”
Yaron nan ya yi shiru yana tunani can ya ce, “Yanzu na gano dalilin da ya sa dukkan gashin Kaka ya ke fari fat.”

Graphic1.JPG

KUSKUREN ADIRESHI
W
ani magidanci ne da matarsa suka sami hutu don haka suka shirya yin tafiya zuwa garinsu, to amma matar tana da wani uzuri don haka sai washegari za ta isa.
Yayin da wannan magidanci ya isa garin ya kama otel, sai ya aikawa matarsa saqo. Yayin aika saqon sai ya kuskure, ya aika saqon ga matar malaminsa wadda mijinta ya rasu kwanaki biyu da suka wuce.
Matar tana tsaye saqon ya shigo, tana karantawa ta yi wata qara sannan ta faxi qasa sumammiya.
Graphic1.JPGMutanen da ke kusa suka shigo cikin tashin hankali suna faxin “Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un, me ya faru?”
Xaya daga cikin matan da suka shigo ta xauki wayarta da ta gani yashe a gefe, ta duba. Sai ta ga an rubuta:
“Matata ki shirya zuwanki inda nake gobe, don na shirya miki komai.”
Wato matar malamin ta xauka mijinta ne da ya mutu ya aiko mata da saqon ya isa lahira, ya shirya mata komai.

TALATIN DA BIYAR
W
ani tsoho ne ya tsinci kuxi, sai ya tafi gidan rediyo ya yi sanarwar ya tsinci kuxi har TALATIN DA BIYAR aka yi cigiya, har aka taki sa’a aka sami wani mutum da ya jefar da kuxi Miliyan Talatin Da biyar ya ji, ya zo gidan rediyon yana ta godiya, aka nuna masa tsohon da ya ce ya tsinci kuxin, ya je ya yi ta yi masa godiya, sannan ya kawo ladan tsintuwa Naira dubu hamsin ya baiwa tsoho.
Tsoho ya karva yana godiya, sannan ya buxe buhun shi ya xauko Naira Talatin da biyar ya miqawa mutumin ya ce, “Na daxe da tsintarsu da har zan kashe sai na ji tsoron Allah na ce bari dai in zo in yi cigiya, kuma ga shi cigiyar ta yi amfani, har na sami toshi mai tsoka.”
Idan kai ne mutumin nan ya za ka yi da tsohon nan?

MUS - MUS MAGE
A
n yi wanisaurayi mai suna Ididiya da ya yi sabon aure, ya je gaida surukansa gidansu da daddare, domin ya nuna godiya ga auren da suka ba shi. Aka sauki Ididiya a falo, duka matan gidan da maigidan da yaran gidan suka zo falon ana gaggaisawa. Bayan sun gaisa, sai maigidan ya sa aka kawo masa abinci da naman kaji zuqu-zuqu.
Aka yi aka yi da Ididiya ya ci abincin nan, amma ya ce sam ya qoshi, sai dai ta ciki na ciki, domin yawunsa ya tsinke. Daga haka sai aka ci gaba da hira ana dariya, shi kuwa hankalin Ididiya yana kan kwanon abincin nan da ke buxe, yana haxiyar yawu. Kawai sai aka xauke wutar lantarki.
Ididiya na ganin haka, ya yi sauri ya xauki cinyar kaza ya kai bakinsa, wal! Kawai sai aka kawo wuta, Ididiya bai gama kai nama bakinsa, kuma ya rabo shi da kwano, gaba xaya kuma hankulan surukansa da ‘ya’yansu ya yo kansa. Ididiya ya rasa yadda zai yi kawai sai ya fara shuna naman yana cewa.
Graphic1.JPG
“Mus! Mus! Mus! Mage, mus muskule mage.”
Surukan nan nasa suka kalli juna, suna shirin yin dariya sai surukinsa ya ce “Malam Ididiya ai a gidan nan babu mage.”
Ididiya ya rasa yanda zai yi sai ya ce “Ai na xauka a gidanmu ne da muke da tarin maguna.”
Suka qyalqyale da dariya.

MUKULLINA NAKE NEMA
W
ani saurayi ne mai suna Tanko ya je zance wajen budurwarsa Nene, bayan da suka gama zancen zai tafi sai ya xauko kuxi Naira dubu xaya ya ba ta, ta qi karva, ya yi ya yi ta karva, amma sam ta qi karva, da ya ga haka, sai ya jefa mata ya juya da sauri ya fita, ita ma ta shige cikin gida da sauri don ya tabbatar ba za ta karva ba.
Can sai saurayin nan ya dawo soron gidan budurwar yana laluben inda ya jefar da dubu xayansa don ya xauka, yana kai hannu daidai wajen ashe itama budurwar ta dawo xaukar kuxin kawai sai ya ji hannu a kusa da nasa hannun, suka ga juna, kawai sai ya yi farat ya ce.
“Ashe ke ce, ai dawowa na in duba xan makullina.”
Itama sai ta ce “Nima xankunnena na dawo dubawa ko a nan ya faxi.”
Tanko ya dube ta ya ce “Ba kin ce min, kin daina sa xankunne ba har sai mun yi aure.”
Nene ta yi murmushi ta ce “Ai kamar ka ce min yau ba da mota ka zo ba.”
Suka yi dariya.

SAI TA KASHANCE ZAN FAXA
W
ani Xanfillo ne suna zaune suna hira shi da abokansa, sai ya hango Kawunsa yana barci a gefen rijiya, kawai sai Xanfillo ya tuntsire da dariya. Abokansa suka ce “Me ya faru kake dariya haka Ja’e?”
Ja’e ya kuma vasgewa da dariya ya ce “Na ga wani abu na shirin faruwa amma ba zan faxa ba sai ta kashence.”
Can sun ci gaba da hirarsu, sai Kawun nan nasa ya afka cikin rijiya ji kake tsundum, kawai sai Ja’e ya kuma tuntsirewa da dariya ya ce “Wallah ta kashence, dama na she sai ta kashence zan faxa.”
Graphic1.JPG
KAI SARKIN FADA QARYA NE
W
ani Alhaji ne yana zaune a qofar gida tare da jama’arsa suna hira. Can Alhaji ya sako wata hira a ciki ya rinqa sharfaxa qarya yana cewa, “A lokacin da muka je Mongoliya can gabashin duniya mun ga wata tsuntsuwa wacce fukafukinta ya kai girman fuloti uku.”
Mutanen Alhaji sai cewa “Wannan haka yake, gaskiya ne wannan.”
Da wani yaron Alhaji ya ga qaryar ta yi yawa, sai shima ya ce “Alhaji har ka tuna min da wata bishiya wacce in aka sareta sai an yi shekara biyar ana amfani da itacen.”
Alhaji ya harareta ya ce “Haba Malam wannan qarya ne ta ya ya haka za ta faru?”
Mutanen wajen suka ce “Gaskiya qarya ne.”
Alhaji ya ci gaba da cewa, “Idan har gaske ne a ina wannan bishiyar take?”
Wannan mutumin ya ce “Yawwa Alhaji, ai wannan tsuntsuwar da ka ba mu labari a wannan bishiyar take da sheqa da ‘ya’yanta.”
Alhaji ya ce “Au to to, haka ne, na gane bishiyar ai in mutum mai tattali ne sai ya kai shekara bakwai ana amfani da ita a gidansa.”

YO SUN IYA WANNAN ABIN ARZIQIN NE
W
ani dattijo ne ya kamu da rashin lafiya, sai aka kai shi asibiti aka duba shi, inda aka kwantar da shi. Don haka sai aka rinqa kawo masa abinci, komai aka kawo masa irin su tuwo da shinkafa da fura duk sai ya ce ba zai iya ci ba saboda rashin lafiya.
Graphic1.JPG
Ana haka sai wani abokin ‘ya’yan wannan dattijo ya zo dubiya, ya ga duk abin da aka ba shi ya qi ci, sai ya ce “To a samo masa hanta mana da qwai da naman kaji a gani ko zai ci.”
Suruf Dattijon nan ya miqe zaune ya ce “To sun iya wannan abin arziqin ne. Ba sai dai su yi ta neman kashe ni da tuwo da kunu ba.”

INA FA ALLAH YA KIYAYE?
W
ata Bafulatana ce ta xauko kayan nono tana sauri za ta kasuwa, ba ta ankara ba ta yi kicivis da wani mutum ta hankaxe shi, nonon ya zube qorai suka fashe. Mutumin nan ya dudduba ya ga nonon bai vata kowa ba, sai ya ce “Kai amma fa Allah ya kiyaye.”
Da jin haka sai Bafulatana ta ce “Haba Malam, ina fa Allah ya kiyaye nonona ya zube.”

BAN NA GOMA...
W
ani Xanfulani ne ya je kanti ya ce a bashi lemon kwalba. Mai kantin ya ce Naira saba’in ne.
“Yo ba zan iya shiya ba ne, maza xauko wa Fullo.”
Aka xauke masa aka buxe masa lemon, yana gani gas ya taso ta cikin kwalba, sai ya yi sauri ya ce “Kai aradun Allah ya yi min yawa, xauko leda ka ban na goma.”

IKON ALLAH, YAU KUMA RUWAN NAMA AKE YI
K
wana biyu da yin babbar sallah wani Kaxo ya kai ziyara gidan surukansa, bayan sun gaggaisa aka kawo masa nama cike da kwano. Sannan aka ba shi wuri. Kaxo ya yi ta gabzar nama ba ji ba gani har ya qoshi. Da ya tashi tafiya ya rasa yadda zai yi, sai ya xauki ragowa naman nan ya sauke hularsa ya juye a ciki.
Sannan ya fito tsakar gida don tafiya, ya durqusa da qyar ya ce “To Inna, Baba ni zan tafi. Allah ya maimaita mana.”
Suka amsa amin. Ya miqe zai tafi sai ga nama yana zubowa ta hularsa, cikin sauri Kaxo ya wage baki yana cewa, “Ikon Allah yau kuma ruwan nama ake yi. Kai Allah mun gode maka.”
Surukan nan nasa suka rasa yadda za su riqe dariya, kawai sauka qyalqyale da dariya.

NA YI MIKI DODO KO?
W
ata rana wani mutum matarsa ta yi yaji, shiru-shiru ba ta dawo ba, har tsawon mako guda, sai ya shirya ya niqi gari ya tafi qauyen matar tasa. Bayan ya isa sun gaisa da surukarsa, ya huta, sai ta kawo masa fura cike da langa, domin ta lura ya jin 'yar bahuwa.
Da fitar surukar tasa sai wannan mutum ya miqe ya leqa, sai da ya tabbatar ta bar wurin, sai ya rinqa tsalle yana rawa yana cewa "In sha fura, sannan kuma a ba ni matata in tafi da ita. Lallai ni mai nasara ne." Yana tsalle bai lura ba, sai ya daki langar furar nan, take ya faxi, fuskarsa ta faxa kan langar nan, fuskarsa ta yi buya-buya da fura.
Hankalinsa ya tashi, ya duba gefe ko zai ga ruwa ya wanke, bai ga ruwa ba, ya duba ko zai ga tsumma ya goge, nan ma babu. Yana cikin wannan halin sai ga surukar tasa ta dawo, ta kawo masa ruwa. Kawai sai ta ga wannan abin mamaki, ta yi turus tana kallonsa cikin mamaki da tsoro.
Shi kuma ganin zamiya ta qare, sai ya dubi surukar tasa ya yi tsuru yana kaxa gashin baki yana faxin, "Na yi miki dodo ko? Na tuna lokacin muna yara ne."
Surukar nan tasa ta saki ruwa ta yi waje tana faxin "Surukin namu ya haukace."

KO'INA AKWAI NA ALLAH
W
atarana wani Alhajin Birni, gogaggen xan bariki ya je wani gidan karuwa don hutawa, sai ya tarar da karuwan gidan da 'yan daudu da manema duk a cikin wani hali, sun yi jugum-jugum, sai ya rava ya tambayi wani mai siyar da sigari da ke gefe ya ce.
"Kai yau me yake faruwa a gidan nan, gidan da na saba ganin ana shargalle da harkoki?"
Mai sigarin ya ce "Ai Alhaji yau kusan sati guda kenan babu harka, babu kuxi a gari babu dalilin samunsu shi ya sa ka ga haka."
Alhajin Birni ya yi dariya ya zaro kuxi ya rinqa rabawa kowa yana cewa "A tashi a sha sha'ani a yi shargalle da kalelesuwa."
Wani xan daudu da ke gefe cikin jin daxi ya dubi Alhajin Birni ya ce "Allah mai iko, a ko ina akan samu na Allah."
Alhajin nan ya harare shi ya ce, "Ni ba na Allah ba ne, na shaixan ne."

MAHASSADANKA FADAWANKA
W
ani maroqi ne ya zo wajen wasu fadawa, ya yi ta roqonsu su ba shi dama ya yiwa sarki kirari ko ya samu 'yar taguwa. Da qyar suka qyale shi bisa sharaxin idan ya samu zai basu wani abu.
Sarki na zaune maroqi ya je ya fara koxa shi Fadawa na cewa "Gaskiya ne wannan."
Maroqi na cewa "Taka gaba salamun xan toron giwa, zamanka lafiya tashinka lafiya mai taqama da girman Allah, kai kaxai gayya..."
Fadawa na faxin "Daidai ne."
Can sai Maroqi ya manta ya ce "Mahassadanka sai sun ji kunya, Xan Marayan zaki, mahassadanka fadawanka Sarki."
Fadawa suka yi caraf suka ce "Hattara mahaukacin Maroqi, ashe ba ka warke ba, hattara, a yi waje da shi."
Suka cafe shi yana zillo suka yi waje da shi.

AKUYAR NAKE YIWA RUKIYYA
W
ani saurayi ne xan qarya, wanda ake kira da suna Xanhutu, kullum idan ya je wajen 'yanmatansa sai ya yi ta zabga musu qarya yana nuna shi wani ne, mahaifinsa mai tarin kuxi ne da sauransu.
A cikin 'yanmata Xanhutu akwai wata mai suna Ladidi, mahaifinta ya ce ta fito da mijin aure, don haka ta yi ta jira Xanhutu bai zo ba, sai ta je gidansu nemansa, tun da aka kwatanta mata gidan ta ga irin gidan talakawa ne sai jikinta ya yi sanyi, amma kuma ba ta same shi ba, don haka watarana sai ta yi sammako ta je da sassafe don tana sa ran samunsa.
A daidai wannan lokacin Xanhutu yana kwance a inda yake kwana a qofar gida, a kan tsohuwar yagaggiyar tabarmar kaba, da wani cuburbuxaxxen tsohon bargonsa, a gefensa kuma akuyarsa ce kwance a jikinsa, daman haka kullum suke kwana. Da Ladidi da qawarta suka zo wajen aka ce musu shi ne a kwance sun yi mamaki, har Ladidi ta yi fushi ta cewa qawarta kawai su tafi, sai qawar ta ce "Ai bai kamata mu zo ba, kuma mu tafi ba tare da mun yi magana da shi ba."
Don haka qawar Ladidi ta fara qoqarin tashinsa, har ya farka, Xanhutu yana tashi da ya lura budurwarsa ce Ladidi kawai sai ya yi sauri ya jawo kan akuyar nan ya dafa ya fara karatu yana cewa "A'uzu billahi minash shaixanir rajim, fita ku fita na ce, ku fita A'uzu billahi...."
Qawar Ladidi ta qyalqyale da dariya, ita kuma Ladidi ranta ne ya vaci ta dube shi ta ce "Me kake yi kenan?"
Xanhutu ya vata rai ya ce "Ruqiyya nake yi mata, kin san muna yiwa mutane da dabbobi ruqiyya, idan zamu yiwa dabbobi ruqiyya dole sai kin ganmu a cikin wannan yanayi na dauxa da qazanta."
Ladidi ba ta san lokacin da ta fashe da dariya ba.

XAN WANKA DA LADAN
W
atarana ne Xanwanka ya shiga gidan wata mata kwartanci, suna zaune suna hira kafin su fara sha'ani, sai suka juyo sallama, suka tsorata, take matar ta ce "Ga maigida nan."
Da sauri ta xaga qasan gado ta ce Xanwanka ya shiga, ya yi sauri ya shige. Sannan ta ba wa mai sallamar damar shigowa, ashe wani kwarton nan Ladan ya zo, ta sauke shi, suka zauna suna hira, ba su daxe da fara hirar ba sai suka jiyo wata sallamar.
Gaban matar ta tashi, domin ta san wannan lokacin Maigidan nata ne ya zo, don haka ta cewa Ladan ya ya za a yi? Kafin Ladan ya yi magana, kawai sai ya Ladan ya xaga qasan gado ya afka.
Kawai sai ya yi kicivis da gashin bakin Xanwanka buyu-buyu a qarqashin gadon. Daman Xanwanka da Ladan ba sa ga maciji, kullum cikin faxa suke. Xanwanka ya harari Ladan.
"Allah ya kamaka yau ka shigo hannuna, sai yadda na yi da kai."
Ladan ya ce "Kai dai Allah ya kama don na san za ka zo, shi ya sa na shigo nan don in kamaka in kawo qarshen iskancinka da rashin mutuncin da kake yi min."
Xanwanka ya ce "To mu fita mu ga wanda aka kama." Ya daqumi kwalar Ladan.
Ladan ya yi sauri ya ce "Kai kai kai, kai wane irin mai taurin kan mutum ne."
Maigida yana tsaye yana jin wannan cacar bakin daga qarqashin gadonsa, sai ya dubi matarsa ya ce "Me yake faruwa a gidan nan ne?"
Matar ta dube shi ta ce "Haba maigida rediyo na kunna ake yin wasan kwaikwayo."
Maigida ya ce "A qarqashin gadon nawa ake wasan kwaikwayo?"
Kafin ya rufe baki Xanwanka da Ladan suka yi wuf suka fito suna cewa "Qwarai kuwa bari ma ka ga yadda ake faxa a wasan kwaikwayon."
Ladan ya zabgawa Xanwanka mari ya ruga da gudu, Xanwanka ya rufa masa baya yana ihu.
Maigida ya saki baki yana kallon abin mamaki.

NAWA NE KUXIN AURE
W
ani saurayi ne yake son aure, ya rasa yadda zai tambayi mahaifinsa, sai watarana suna zaune, sai ya yi dabara, ya ce "Abba wai ko kuxin aure suna kaiwa nawa?"
Mahaifin nasa ya dube shi ya kawar da kai ya ce "Ban sani ba."
Yaro ya yi mamaki, ya ce "Abba ya kamar ba ka sani ba?"
Mahaifin ya yi dariya ya ce "To ai har yanzu biya nake yi. Ko ba ka ganin kullum sai na ba mahaifiyarka kuxi."

DA FATAN BA KA KALLON NAWA
A
wata makarantar boko, Malamin lissafi ya rubutawa xalibai jarabawa, sai ya ke kewayawa don kar a samu wani ya satar amsa. Sai ya hango Isa kamar yana leqa littafin Ali da ke zaune kusa da shi, sai ya dube shi ya ce, "Isa da fatan ba jarrabawar Ali kake leqawa ba?"
Isa ya kalli Malam ya ce "Kai ma Malam da fatan ba tawa jarrabawar ka leqa ba."

AI SHI YA SA NAKE KUKAN
W
atarana wani magidanci da matarsa suna kwance, kawai sai matar ta yi mafarki, sai ta tashi tana kuka, maigidan ya tashi hankalinsa a tashe yana tambayarta.
"Uwargida me ya faru ki ke kuka da tsakar daren nan?"
Sai matar ta kada baki ta ce, "Mafarki na yi wani hamshaqin maikuxi ya sace ni, ya gudu da ni."
Maigida ya yi murmushi ya ce, "Ki daina kuka ai mafarki ne kawai."
Graphic1.JPG
Matar ta harare shi ta ce, "Ai saboda mafarki ne shi ya sa nake kuka, ina ma gaske ne."
Idan kai ne maigidan ya za ka yi?

MISS CALL
W
ata mata ce kullum idan tana waya sai ta yi awa bakwai awa takwas zuwa goma sha tana waya, kullum cikin karvar kuxi take a wajen mijinta don ta sayi katin waya. Haka nan idan aka kirata a waya ma sai ta yi sama da awanni ashirin suna waya.
Da mijin ya gaji da wannan cacar kuxin sai ya sata a gaba ya kai ta wajen iyayenta suka yi mata nasiha don ta daina.
Washegari suna zaune suna hira, sai ga kira ya shigo wayar wannan mata, ta xauka tana duban mijinta, sannan ta koma gefe tana magana. Cikin ikon Allah wannan lokacin ba su fi mintuna arba'in ba ta kashe wayar.
Mijin ya yi murmushin jin daxi, don da alama matar tasa ta ji faxan iyayenta, ya dubeta ya ce "Yau ba ki daxe a waya ba, kin ji nasiha kenan."
Matar ta yi dariya ta ce "Ai miss call ne."

To mu haxu a littafin ABOKIN DARIYA da GIDAN DARIYA da 'YA'YANMU
NakuKabiru Yusuf Fagge (anka)
07030319787

NEMI LITTAFAINA
·         KAI MA KA DARA 1-2
·         GIDAN DARIYA
·         LABARIN SARKIN KARYA
·         ABOKIN DARIYA
·         MALAMIN BAN-DARIYA
·         LABARUN HIKAYA DA HIKIMOMIN HAUSAWA
·         TATSUNIYOYI DA LABARUN HIKAYA
·         ZUNBULI KAKAN MAROWATA
·         MU KOYI KARATU 1,2,3
·         ‘YA’YANMU
·         DABARUN RUBUTA KAGAGGUN LABARAI
NA KU:      KABIRU YUSUF FAGGE (ANKA)
07030319787
Nemi littafin'YA'YANMU
'ya'yanmu.JPG
Domin ka sha labarin ban tausayi, mamaki da ban haushi na 'ya'yan Hausawa.
 


No comments:

Post a Comment

RANAR HAUSA: ƘUNGIYAR HAUSA TA BUK TA CIRI TUTA

 RANAR HAUSA: ƘUNGIYAR HAUSA TA BUK TA CIRI TUTA Nabila Muhammad Ƙungiyar Hausa ta BUK ƙarƙashin jagorancin Kabiru Yusuf Fagge wanda aka fi ...