Wednesday, May 27, 2020

KUDIN KORONA



KUDIN KORONA
Gajeren Labari
Rubutawa: Kabiru Yusuf Fagge

Na yi sharkaf da gumi, saboda irin yadda tun safe nake ratsa unguwanni da kasuwanni a cikin rana, abin ne ya hadar min goma da ashirin, ga rashin kudi, ga rana, ga shi mutane sun ki siyen maganin beran da nake tallan.
A wannan hali da ake ciki mutane ba ta maganin bera suke yi ba, ta abincin da za su ci suke. Fatan da nake yi in samu wadanda ko tayawa su yi in karyar musu in sami abin da zan ci ni da iyalina.
A kwanar shiga unguwar Fagge, n a ji wasu matasa suna hira, hirar ta ja hankalina na koma gefe na rakube ina sauraronsu.

"Da farko duk mutum daya mai cutar Korona idan yana da iyali za a kai mi shi kayan abinci, buhungunan shinkafa da taliya da sauran kayayyaki, sannan kuma ana ba shi N80,000 a kullum..."
Ban gama jin karashen zancen ba na tashi ai guje tare da yankewa zuciyata abin da zan yi.
"Gida zan je, in ajiye kayana, ina da lambar hukumar NCDC in kira su, su zo, su tafi da ni, don a killace ni."
A gida ban yi wa matata bayani ba, na ari N100 a wurinta na sa a wayata, na fara kiran lambar hukumar, amma na yi kira ya fi sau shurin masaki ba a dauka ba. Dole na gaya wa Hauwa halin da ake ciki.
"Haba maigida kawai don kana mura da zazzabi sai ka kai kanka wurin nan a zo ana kyamar mu. To wane ne baya yin murar..."
"Tawa ba irin taku ba ce, ke dai ko da an zo gare ku, ki ce sati na daya a killace a daki, yau ne ana kira ba a zo ba, shi ne na tafi." Na ce mata, tare da kwantar mata da hankali.
"Ai shi ke nan. Batun abinci fa?"
"Za a kawo muku."
"Wane ne zai kawo, aikowa za ka yi?"
"HUkuma da gwamnati ne za su kawo, ki kwantar da hankalinki, haka ake yi wa duk wanda aka killace."
"To ko dai akwai abin da kake shiryawa ban sani ba?"
"Ba wani abu, bari in je kar ki bata min lokaci."
Na fita da sauri. Daga unguwar Koki zuwa asibitin Malam Aminu Kano inda ake killacewa tafiya ce mai nisa, kuma ga shi ba ni da kudi. Amma faduwa ce ta zo daidai da zama, a kasa na tafi, domin yin hakan ma wata ribar kafar ce.
Ina zuwa, na tambayi bangaren 'yan koronar, daga nesa-nesa aka nuna min, na isa wajen wujiga-wujiga da ni, likitar da ta gan ni, tun kafin in kammala bayani ta tausaya min,  nan aka shiga auna ni, take aka tabbatar temperature ta, ta yi sama, kuma ian tare da korona.
Na yi dariya a raina, na ce "Ba su san tsabar dukan sayyada da yunwa da tension ne suka harzuka temperature tawa ba, suke ganin kamar ina da koronar."
Bayan rubuce-rubuce na suna da inda nake da sauransu aka ba ni gado, tare da hada ni da abinci.
Lokacin da na kammala cin abinci na nutsu da a ce a lokacin za su sake auna ni da za su tabbatar kalau nake don tuni temperature ta din tawa ta sauka. Sai lokacin ma na lura da mutane ukun da suke dakin, daya dattijo ne, biyu matasa, suna kallona. Daya ne daga matasan ya matso kusa da ni.
"Kai ma an kawo ka ke nan?" Ya ce da ni.
"A'a, ni na kwo kaina."
Suka yi min wani irin kallo.
"E mana, ni na kawo kaina don in tserar da wasu."
Zancen nawa bai kai zuci ba.
Bayan kwana biyu, ban ji zancen kudi ba. Na fara tunanin ko dai sai mun yi mako biyun za a hada mana a ba mu. Ban yi zurfinc iki ba, na tambayi daya saurain nan mai suna Nazifi.
"Wai ba kullum ake biya ba?"
Nazifi ya kalle ni.
"Kullum ana cirewa duk mai cutar wasu makudan kudi."
"Yawwa, to yaushe ake bayarwa?"
"Malam ba kai za a bai wa ba. Ni dai na san ana cirewa ko kakshewa duk wani mai korona kudaden nan, watakil haka ake kashewa mutum ke nan."
"To me ake kashe mana? Tun da na zo ni dai na san ana ba ni abinci mai kimar, N250 sau uku sai kuma bitamin C da ake ba mu, mu sha, da shawarwarin kare lafiya da ake gaya mana, ko ana mana abin da ya wuce hakan?"
"Wadannan abubuwan da ka lissafa su ne naka, sauran na masu aiki ne da wadanda ba mu sani ba. kai dai tund aan kai ma abinci gida, to Allah ya ba mu lafiya."
"NI kam lafiya ta lau." Na ce a raina, "Kawai ina fama da rashin lafiyar aljihu ne, na so na magance ya sa na kawo kaina, ashe akwai wadanda suke gabana masu son magance matsalar aljifansu."
Wannan ma a zuci na yi ta fada, ashe zancen ya fito fili.
Suka kyalkyale da dariya, Dattijon ne ya yi magana.
"Yaro idan kai sammako ka yi to mutanen nan a tafe suka kwana. Maganar gaskiya, duk mutum daya ana kashe masa kudi da yawa a matsayin mara lafiyar korona, inda kudin ke tafiya ne ni ban sani ba, sai Allah."
Ya dan yi shiru.
"Dazu na ji a labarai gwamnatin jihar Lagos na cewa, tana kshe N50,000 ga gwaji na kwoane mutum daya da yake da cutar. Sannan kamar yadda kake tsammani, kuma kowa yake fada a kullum ana ware makudan kudade ga mai cutar tare da kashewa a rubuce ba aikace ba." Daya saurayin ya ce.
Ina shirin yin magana, Dattijo ya riga ni.
"Ai kai dai ka zama kadara, ka gode Allah za ka tsira da kayan abinci da aka kai gidanka."
"Ai kuwa wallahi guduwa zan yi."
"A banza don kuwa ka riga, ka shiga cikin lissafi, ka hutar da su."
Muka yi jugum cikin damuwa.

-Kabiru Yusuf Fagge.

1 comment:

RANAR HAUSA: ƘUNGIYAR HAUSA TA BUK TA CIRI TUTA

 RANAR HAUSA: ƘUNGIYAR HAUSA TA BUK TA CIRI TUTA Nabila Muhammad Ƙungiyar Hausa ta BUK ƙarƙashin jagorancin Kabiru Yusuf Fagge wanda aka fi ...