Friday, March 20, 2020

UBANKI YANA GIDA YARINYA - Gajeren Labari




UBANKI YANA GIDA YARINYA
(Gajeren Labari)
Kabiru Yusuf Fagge

Ina zaune a cikin Keke Napep muna tafe, don kai ziyara wajen abokina Hakimin Wajila, mai suna Iro Mamman, kida ne kawai yake tashi a Napep din, a wakar Lalakukulala, mai jan Napep din dattijo ne da ya doshi shekaru hamsin zuwa hamsin da biyar, don ga furfura da gemu nan a tare da shi.
Sai gyada kai yake kamar kadangare, wani lokacin har wani zabura yake ya kwaso Shoki a waje, sannan ya hankado shi cikin motar, ni kam kallonsa kawai nake.
A daidai kwanar shiga unguwar Wajilar, wata kyakkyawar yarinya 'yar birni, mai dauke da shekaru 15 zuwa 16 ta tsayar da mu.

"Wajila za ka kai ni."
"Hau mu je 'yanmata, kudinki Naira 50."
Ta hau, muka fara tafiya. Ko nisa ba mu yi da daukar yarinyar nan ba, ta sake yin magana.
"Baba kai ma kana jin ire-iren wadannan wakoki na 'yan-bana-bakwai."
Wani irin ihu mutumin nan ya yi, sannan ya yi gefe da motar, ya juyo, ya kalli yarinyar.
"Kuturun uban nan kayyasa! Yarinyar wane ne Babanki. Ai ubanki yana gida."
"Ni kuwa na fadi haka ne don girmama furfurar da ke kanka, da kuma gemu." Ta ce da shi.
"E, shekaru ne suka kawo wadannan abubuwa da kika fada, amma ki sani, yanzu na fara cin duniyata, don kuwa a yadda nake gani yanzu ni sa'anki ne, ba ni da aure, kuma ba zan yi ba a nan kusa, sai ma kin riga ni yin aure, don sai na gama cin duniyar tawa. Saboda haka ki rinka sanin wane ne Babanki, ko kuwa haka shi ma baban naki yake? "
"Gaskiya ba haka mahaifina yake ba."
"To, don haka Babanki yana gida, ki daina ganin kowanne tsoho kina ce masa Baba."
"Haka ne. Na daina."
Lokacin da na kyalkyale da dariya, a lokacin shi kuma ya zaro sigari ya banka mata wuta, bayan ya yi doguwar tsuka, ya karkace, ya tuttulo mata hayakin a fuskar.
Haka kawai, na kasa cewa komai sai kallon ikon Allah. Ya dora da cewa.
"Mu je ko kina da magana kawata?"
A sanyaye ta amsa, "Mu je kawai Malam."
"Kan uba. Wane ne Malam din?" Ya sake amsa mata.
Ta marairaice, "Don Allah ka yi hakuri, ba kai ba ne. Kuma na daina. Mu je Dancaburos."
"Good! Girl, ko ki ce Caburos, ko ki ce Baabaa shi ne sunana. Hakan ya sa an yafe miki kudin motar ba."
Ya fincike mu, ya yi gama yana rausayawa har da kwaso Shokinsa, babu abin da ya dame shi.

1 comment:

  1. Hahahaha lalle kuwa ga Baabaa🤣🤣🤣

    ReplyDelete

RANAR HAUSA: ƘUNGIYAR HAUSA TA BUK TA CIRI TUTA

 RANAR HAUSA: ƘUNGIYAR HAUSA TA BUK TA CIRI TUTA Nabila Muhammad Ƙungiyar Hausa ta BUK Æ™arÆ™ashin jagorancin Kabiru Yusuf Fagge wanda aka fi ...