Friday, January 4, 2019

Short Story: NI MA HAKA NAKE!


NI MA HAKA NAKE!
Gajeren Labari

(c) Kabiru Yusuf Fagge (anka)
Ina isa wajen dan restaurant din na yi kici6is da wata kyakkyawa mace wadda ta sha hoda da gazal da jan baki tana yi min murmushin sace zuciya da ilahirin jiki.
 
Ban yi kasa a gwiwa ba ni ma na mayar mata da lallausan murmushi, don an ce yaba kyauta, tukwici.
To amma kuma me zai faru? Ban yi aune ba, na ji saukar wani wawan mari a kuncina na dama, har sai da na daina ji da kunnen bangaren na mintuna biyar, idona daya ya kanne. Bayan na warware ne, na juya a tsanake, na kalli gwanin da ya sharara min wannan mahaukacin marin.
Wani tikeken kato na gani tsaye a kaina yana huci, cikin zubar kwalla na ce, "Bawan Allah me na yi maka, ka yi min wannan marin?"
Ya nuna matar da muka yi musaya murmushi da ita, "Wannan matata ce, me ya sa ka yi mata murmushi? Na ga lokacin da ka bi ta da murmushi."
"To amma Bawan Allah, ba ka ga lokacin da ita ta fara yi min murmushin ba."
Ya yi dariya, "Ai ita haka yanayinta yake, haka fuskarta take, saboda tsabar kyanta, duk wanda ta kalla sai ya ga kamar murmushi take yi masa...."
Bai rufe baki ba, ni ma na takarkare tun karfina na sharara masa mari, sannan ban tsaya bata lokaci ba, na ci gaba da cewa, "Idan haka yanayinta yake, ni ma haka nawa yanayin yake, duk wanda na kalla sai ya ga ina murmushi idan ya yi tunanin murmushin nake, idan kuma ya yi tunanin fushi nake, sai ya ga kamar ina kuka..."
Mamaki ya kama shi, mamakin ya aka yi dan firit da ni, na iya zabga masa mari haka, yana cikin tunanin irin matakin da zai dauka, wasu sojoji guda uku suka iso wajen suna kallona, "Ya aka yi Anka ashe har ka riga mu zuwa."
"Alhamdulillahi." Na furta a raina, a fili kuma ina kallonsu, na ce "Wallahi na iso, ai dole in zo da wuri, don amsa gayyatar Babban Maigida."
Suka yi dariya, muka tafi, ina yiwa kato mai mata gwalo, shi kuma yana cije baki.


No comments:

Post a Comment

RANAR HAUSA: ƘUNGIYAR HAUSA TA BUK TA CIRI TUTA

 RANAR HAUSA: ƘUNGIYAR HAUSA TA BUK TA CIRI TUTA Nabila Muhammad Ƙungiyar Hausa ta BUK ƙarƙashin jagorancin Kabiru Yusuf Fagge wanda aka fi ...