Sunday, January 13, 2019

TALAKAWA SUN FI YIN AURE





TALAKAWA SUN FI YIN AURE
Labari
(c) Kabiru Yusuf Fagge 


An tambayi Sheikh Abu Yusufa Alfagawy cewar, "Aure a kasar Hausa yana da tsada, to amma me ya sa sau tari talakawa sun fi yin aure da yawa fiye da masu hannu da shuni. Kuma sun fi yin saki fiye da masu hannu da shuni..."
Sheikh Alfagawy ya murmushi ya ce, "Ai idan ka ji an ce an yi da yawa dole a yi sakin da yawa. To amma Alhamdulillahi, na yi farin ciki da wannan tambayar taka matuka, ba don komai ba, sai don irin wannan abu ya shafe ni sosai, kuma na sami kaina a cikinsa, wato..."
Ya fara ba da labari.

"Maganar gaskiya yawancin matan da muke aure a al'ummar Hausa sun fi baiwa kudi ko abin hannu daraja fiye da soyayya ko zaman rayuwar aure don Allah. Da zarar sun fuskanci da kyar kake kawo rabin kwanon shinkafa ko kasa da haka gida, sannan suka fahimci sai sati-sati ake surka abin miya wato nama, to za su zabtare kashi bakwai da rabi na biyayyar da suke yi maka, idan a farkon aurenku tana yi maka wasu abubuwa da yawa na biyayya, to kuwain sha Allahu watanni tara na giftawa za ta rage sama da rabi na daga biyayyar da take yi makan," ya yi gyaran makogoro. Sannan ya dora.
"Haka ne ya faru da ni, da matata, mai suna Salaha, saboda ba na son in yi saki nake zaune da ita, amma abubuwan da ta yi min da tuni na aunata waje...
"Ina ba ka labari, wato sannu a hankali, muna zaune da ita tana yi min yadda take so, ni kuma ba ta yi min yadda nake so, yau da gobe Allah ya yi min arziki, na mallaki motoci da gidaje, abin da nake gaya maka, za ka sha mamakin idan na ce maka wallahi a yanzu biyayyar da take yi min kamar ta fi kowa iya biyayya a cikin matan duniya, kuma kamar in bude aljanna in watsa ta a ciki...
"To amma da farko, na dade ina mamakin a ina ta koyo wadannan abubuwa na kyautatawa a yanzu, tsaf da na yi tunani, sai na gano cewar masu gidan rana take yiwa ladabin ba ni ba..."
Ya yi murmushi, kana ya ci gaba da cewa, "Maganar gaskiya masu kudi suna samun biyayya daga matansu saboda suna da abin hannu, idan ki ka yi masa rashin mutunci ko ki ka ki yin biyayya yanzu zai auro wata ko da kuwa bai sakeki ba, wannan tunanin da kuma tunanin idan ya saketa ba ta san hannun da za ta fada ba, ya sa suke yin biyayya yadda ya kamata...
"Kuma ka sani shi wannan mai kudin ko wata ya aure, zai dai su yi ta yi masa biyayya a zahiri, amma a badini akwai abin da suke yiwa biyayyar.
"Ita kuma macen da take auren talaka gani take yi ko ya saketa, ko ya karo mata kishiya duk shammakal. Don haka shi kuma talaka da ya rasa kulawar da ya kamata ya samu a wurin matarsa, da zarar ya sami faraga sai ya ga ai gwara ya auro wata ko ya samu kulawar da ya rasa, ko kuma ya koya mata yadda ya kamata ta zauna da shi, tun da wannan ta ki bi.
"Idan aka sami akasi, wani na iya korar matar tasa, wani kuma zai ci gaba da hakurin zama da ita don ko ta yi koyi da wadda ya auro din, idan itama ba ta bijire daga baya ba...
"Fata dai anan shi ne, Allah ya sa matan su fahimci wannan mas'alar su gyara, don a samu daidaito, Allah ya sa mu gyara." Ya tsahirta kafin ya dora da cewa, "Akwai wata tambayar?"


No comments:

Post a Comment

RANAR HAUSA: ƘUNGIYAR HAUSA TA BUK TA CIRI TUTA

 RANAR HAUSA: ƘUNGIYAR HAUSA TA BUK TA CIRI TUTA Nabila Muhammad Ƙungiyar Hausa ta BUK ƙarƙashin jagorancin Kabiru Yusuf Fagge wanda aka fi ...