Tuesday, January 15, 2019

Short Story: ADDU'AR MAKABARTA



ADDU'AR MAKABARTA

Gajeren Labari
(c) Kabiru Yusuf Fagge (anka)
Da zarar an binne mamaci kamar yadda shari'a ta tanadar, to ana bukatar kowa ya watse yana mai yi masa addu'ar samun rahama, face 'yan'uwan mamaci da za su tsaya su yi masa addu'a da tuni ga ababen shaidawa da gaskiya don tambayar kabari, sai kuma wadanda za su iya tsayawa don yi wa iyalai da 'yan'uwan mamacin addu'a.

A ranar da muka kai Marigayi Adam Mai Dinki, tun kafin a binne shi na hango Alarammomin unguwarmu su uku, wato Alaramma Malam Zakari Mai-Buhun-Salati da Alaramma Malam Habu Mu-Cika-Da-Addu'a da Malam Kwana-Sallah a rukuni guda, na tabbatar yau idan ba mu yi wasa ba sai mun yi rabin wuni a makabartar nan suna yi mana addu'a.
Iya sanina da su Alaramma da zarar an kammala binne gawar nan idan suka fara addu'o'i suna yi, suna mika wa juna fasin (passing) to sai kowa ya gaji.
Ba zan manta ba, wata hudu da suka wuce, wata yarinya ta rasu, muka kawo ta, ana kammala binne ta, Alaramma Mai Buhun-Salati ya fara addu'a, ya fadi a karanta Kulhuwallahu kafa goma sha dai-dai ya fi sau bakwai, Falaki Da Nasi ma haka, ya zarce zuwa su Ya Shafi, Ya Salamu, Ya Azizu sun fi cikin carbuna takwas-takwas, haka Salatil Fatih kamar muna Musaffa, kai a ranar har da ayoyin da ba na rahama ko gafara ba ma sai da Mai Buhun-Salati ya sa muka biyo, ya tsahirta kuma ya sawa Malam Mai-Kwana-Sallah fasin, shi ma ya yi ta yi, tun muna gumi a makabartar nan har guminmu ya fara kafewa.
Ina kammala wannan tunanin, na fara tunanin to mene ne mafita a yau, don ga manyan sitirakokin (strikers) addu'a suna jiran a gama binnewa su fara - kuma ga rana ta kwalle sosai. Take na fara tunanin kawai na sumame, na gudu, na bar makabartar, ko banza ina mugun jin yunwa, ga rana.
Sai dai kuma, da na dubi tarin mutanen da ke tsattsaye a cikin makabartar, sai na ga idan na gudu ban yi musu adalci ba, ta yiwu akwai da yawa da suka fi ni uzuri.
Ina cikin wannan tunani na ji muryar Alaramma Mu-Cika-Da-Addu'a na fadin, "Mu yi salati goma-goma...ga Annabi...." Da karfi ya fada.
A rikice na dawo da hankalina gurin, na kalli bakinsa yana ta mutsul-mutsul, take cikin ikon Allah wata dabara ta fado min. Kawai, sai na ji ya ce, "Mu yi Kulhuwallahu kafa bakwai-bakwai." Ban jira ba, na amsa masa, ina mai daga murya fiye da ta shi, na ce "Kulhuwallahu kafa bakwai-bakwai, Allah ya yi masa rahama..."
Ya kalle ni, ya yi murmushi, don ya samu wanda zai rinka isar da sakon addu'ar tasa da karfi. To a daidai lokacin na shammace shi na daga murya na ce, "FATIHA!!!" tare da shafawa.
Ai kuwa, duk mutanen da ke wurin suma, suka amsa, suka ce "Fatiha!!!" a tare, sannan suka shafa, suna hamdala, wasu suka dauki hanyar fita daga makabartar cikin jin dadi, wasu suka fara yiwa iyalan mamacin ta'aziyya.
Ni ma hanyar fitar na nufa a sukwane don na san na yi wa su Alaramma kancal, ta gefen ido ina hango su a tsugunne sun yi jangwam da su kamar murafun takwane, suna yiwa juna kallon-kallo a lokaci guda suna hango ni ina sauri, idanunsu jawur kamar su yo tsalle su dirar min, amma ba hali.
Na fita, ina murna,  sai dai na san zan sha mita da kumfar baki a unguwa daga wajen su Alaramma, amma a banza, tunda na sa an fita hakkin mutane, sai dai in ce Allah ya sa mu gane, mu bi sunnar ma'aiki mikakkiya, amin.

No comments:

Post a Comment

RANAR HAUSA: ƘUNGIYAR HAUSA TA BUK TA CIRI TUTA

 RANAR HAUSA: ƘUNGIYAR HAUSA TA BUK TA CIRI TUTA Nabila Muhammad Ƙungiyar Hausa ta BUK ƙarƙashin jagorancin Kabiru Yusuf Fagge wanda aka fi ...