Wednesday, December 12, 2018

HALACCIN MAI MARTABA SARKIN KANO GA MARUBUTA





KANO LITERARY WEEK
HALACCIN MAI MARTABA SARKIN KANO GA MARUBUTA
Ga marubutan da ba su ji bayanin Sarkin Kano ba.

Da farko, duk dalibin da ya yi asarar wata gagarumar lakca mai matukar muhimmanci zai ta bibiya don a gaya masa yadda lakcar ta gudana, ko don dai ya ci jarrabawa ko kuma don ya kara lilimi.
Da yawa marubuta suna ta son su ji me mai martaba Sarkin Kano ya ce a taron marubuta. Mu marubutan da muke wurin gaskiya mun gode Allah, mun gode Manzon Allah (S.A.W.), mun gode wa Sarkin Kano.

Da farko, kafin jawabin Sarkin, marubuta sun ga kauna miraran daga Mai Martaba Sarkin Kano Malam Muhammadu Sanusi II yadda ya jingine dukkanin wasu abubuwa da tarurruka da ke gabansa, ya halarci taron marubuta kuma ya zauna da marubuta tsawon lokaci cikin nutsuwa da soyayya garemu talakawansa.
Abu na biyu Mai martaba Sarkin Kano Malam Muhammadu Sanusi II ya yi jawabi na isasshen lokaci a nutse da ya sa kowanne mahalarcin taron ya nutsu, a ilimance, ya ilimantar da kowa, kuma a gamshe ya gamsar da kowa.
Mai martaba ya hasko kafatanin matsalolin rayuwar Hausawa da hanyoyin gyarasu, sannan ya dora alhakin wani bangare don taimakawa a gyara na wadannan matsalolin ga marubuta, don a sami ingantacciyar al'umma nan gaba.
Mai martaba ya kasa jawabin nasa kamar haka:
ILIMI
"A kwanaki jami'ar Maiduguri ta yi wani bincike da nazari ta gano yadda jihar Legas ta yiwa jihohin arewa fintinkau ta fuskar ilimi, wadda ko da an tashi haikan ana neman ilimin to sai an shafe tsawon shekaru dari biyu kafin a kamo su..."
Tirkashi, dole kowa ya nutsu, sannu a hankali mai martaba ya zayyano wasu hanyoyi ga marubuta da masu sarauta (masu mulki) da hukumomi da za su bi a inganta ilimi kuma a wayar da kai dangane da yadda za a sami ilimi ga yankin Arewa, ta yadda kowane bangare zai ba da tashi gudunmawar don ganin haka ta cimma ruwa.
Sannan sai batun karfafa gwiwa wajen koyar da fannonin ilimi da harshen Hausa, ya kawo misalai da dama cewar duk wasu kasashe suna koyar da iliminsu ne da yarukansu ta yadda mai koyo zai yi saurin fahimta.

BATUN AUREN WURI DA TSARIN IYALI
Mai martaba ya yi cikakken bayanin yadda za a inganta rayuwar iyali ta yadda za a samar da ingantacciyar al'umma akasin wacce ake ciki a yanzu. Ya fito da hanyoyi da marubuta za su isar da wannan sakon cikin rubuce-rubucensu.
Ya yi bayanin yadda za a gujewa samar da matasa da ake amfani da su wajen harkokin daba da yawan sake-saken aure, da yadda wasu mazan suke dukan mazajensu.
Hakika Mai martaba Sarki Malam Muhammadu Sanusi II ya nuna wa marubuta gata, ya ilimantarsu, kuma marubuta suna godiya ga sarki, Allah ya ja da ran sarki, Allah ya saka da alkhairi.
Sannan marubuta suna godiya ga Hajiya Sa'adatu Baba, da take zama tsani tsakanin marubuta da mai martaba, Allah ya saka da alheri.

 


No comments:

Post a Comment

RANAR HAUSA: ƘUNGIYAR HAUSA TA BUK TA CIRI TUTA

 RANAR HAUSA: ƘUNGIYAR HAUSA TA BUK TA CIRI TUTA Nabila Muhammad Ƙungiyar Hausa ta BUK ƙarƙashin jagorancin Kabiru Yusuf Fagge wanda aka fi ...