Friday, July 17, 2020

GUDUMMAWAR MARUBUTA A SHIRIN FIM A TAKAICE - Ado Ahmad Gidan Dabino MON




GUDUMMAWAR MARUBUTA A SHIRIN FIM

A Takaice

Ado Ahmad Gidan Dabino MON

Gabatarwa

Ta hanyar rubutu ne marubuta suke fitar da abubuwan da suke cikin zuciyoyinsu, wadanda suka faru da kuma wadanda suke hasashen za su faru nan gaba, don jama’a masu karatu ko sauraro ta hanyar rediyo su ji ko masu kallo kuma su karu da abubuwan da ke cikin rubutun wanda ya shafi ilmantarwa ko tarbiyyantarwa ko nishadantarwa ko kuma akasin haka.

Rubutu rayayyen al'amari ne da kan wanzu matukar wanzuwar duniya, kuma tamkar shuka ce wadda in har an yi ta za a girbi abin da aka shuka.

Wane ne Marubuci?

 MARUBUCI DAN BAIWA NE, haihuwarsa ake yi ba yin sa ake ba. Marubuci shi ne wanda ta hanyar amfani da fasahar rubutu yakan kirkiri wani yanayi na gaske ko na almara ko tunani ya kuma yi amfani da shi don gina wasu mutane da abubuwa wadanda yake amfani da su don isar da sako ga al'ummar da ke karatun rubutunsa. Shi wannan sako ana tsara shi ne ta hanya ta musamman mai cike da hikima da hazaka don isarwa a saukake, kamar ta hanyar yin amfani da haruffa zuwa kalmomi zuwa jimloli zuwa sidarori da shafuka har zuwa cikakken littafi.

Wani ana haihuwarsa da rubutu wani kuma koyo yake yi, amma duk marubuta za mu kira su. Shi marubuci mutum ne na daban, ba wai ya fi sauran rukunonin bil'adama ba ne, a a, shi dai daban yake da sauran mutane, wato dan baiwa ne. Marubuci na yin tunani ne iri na daban, yana kuma kallon rayuwa da al'amuran rayuwa da wata irin fahimta tasa ta daban, sannan ya bayyana ta a rubuce. Kamar yadda aka ambata a sama shi marubuci dan baiwa ne, sannan shi kansa rubutun baiwa ne.

 

Mece ce Gudummawa?

Muwa wata mata ce mai tabin hankali wadda take tafiya gudu-gudu sauri-sauri, idan ta zo ta tarar da mutane sai ta ba su kyautar abin da ta zo da shi amma fa tare da ita za a cenye abin, wato za ta zauna a ci abin tare da ita, idan ta ga ya kare sai ta tashi ta tafi, wannan ita ce al’adarta kuma kowane lokaci haka take yi wa mutane, daga nan shi ne idan mutum yana so ka ba shi taimako wanda yake sa ran nan gaba shi ma ya saka maka ko kuma nan gaba kai ma ka amfana daga abin, ko kuma Allah ya saka maka, sai ya ce wane me zai sa ba za ka yi min irin gudun da Muwa take ba, daga nan ne mutane suka juya kalmar ta koma gudummawa kai tsaye. A dunkule kalmar gudummawa tana nufin taimakawa da wani abu wanda kake sa ran samun sakamako a nan duniya ko kuma lahira, wata kuma gudummawar ba a samun sakamako sai dai a lahira.

 

Mene ne Fim?

Fim tantagaryar kimiyya da fasaha ce, kuma rayuwar dan’adam ce ake nunawa. Fim yana dauke da tarihi da dabi’un jama’a da muhallinsu da abincinsu da kuma suturarsu. Fim yare ne da kowane mutum yake iya fahimtarsa a duniya, musamman bisa harshensa da tsarinsa na rayuwa da hanyoyin tunaninsa da suka hada da gani da ji da motsi.

Har ila yau, fim hanya ce ta sanarwa da ilmantarwa da jan hankali da nishadantarwa da fadakarwa da yada manufa da tallatawa. A dunkule kafa ce daga cikin kafafen yada labarai, sannan kuma hanya ce ta kasuwanci.

 

Wace Irin Gudummawa Marubuta Suka Bayar a Harkar Fim?

Kacokan zan mayar da maganar ne a kanmu wato masu shirya finafinan Hausa na asana’antar Kannywood, ba na son in shiga wata uwa duniya gwara in tsaya iya inda muke muka fi fahimta, muka fi sani muka fi wayo domin mu fi saurin kamo bakin zaren. Kuma za mu yi a takaice saboda nan ba fage ne na Jami’a ba, wajen taron ga-ni ga-ka wanda za a baje koli ido da ido ba a yi bayanai da baki da baki ba.

 

Kafuwar Kannywood

An kafa wannan masana’anta ne tare da marubuta, marubutan kuma na littattafai ko in ce labarai. Wasu daga cikin mu za su iya tuna lokacin, a wajejen shekarar 1994 zuwa 1995 aka yi yinkurin kafa Kungiyar Masu shirya Finafinai ta Jihar Kano, wato Kano State Film Makers Association. Mutanen suna da yawa amma wasu daga ciki da zan iya tunawa a wannan kokari su ne:

1. Ibrahim M. Mandawari

2. Adamu Muhammad Kwabon Masoyi

3. Aminu Hassan Yakasai (Marigayi)

4. Auwalu Muhammad Sabo

5. Auwalu Mashal

6. Dan’azumi Baba Chediyar ‘Yan Gurasa

7. Bala Anas Babinlata

8. Ado Ahmad Gidan Dabino, MON

9. Balarabe Sango II

 

In muka dubi wannan jerin sunaye, za mu ga sama da rabin mutanen marubuta ne, kuma duk suna da littattafai ko labarai da suka rubuta a lokacin da suka yi wannan gangami na kafa kungiyar masu shirya fim ta farko.

Yi wa fim Jaket: Wanda ya fara yin sa shi ne Bala Anas Babinlata a shekarar 1995. Kafin ya gabatar da wannan tunani, ba a sanya wa fim jaket sai da ya kawo wannan abu ne aka amsa ga shi har yanzu ana yi wa fim jaket.

Samar da sunan Kannywood a shekarar 2002, Sunusi Shehu Daneji shi ne ya samar da wannan suna kuma marubuci ne na.

 

Marubuta da Suka Fara Kafa Kamfanonin Shirya Finafinai Kuma Suka Zuba Jari

Ga wasu daga cikin marubuta da suka bayar da gudummawa wajen kafa kamfanonin shirya finafinai a wannan masana’anta ta Kannywood, sannan kuma suna rubutawa suna shiryawa suna bayar da umarni.

1. Ibrahim Mandawari

2. Aminu Hassan Yakasai (marigayi)

3. Bala Anas Babinlata

4. Dan Azumi Baba Chediyar ‘Yan gurasa

5. Ado Ahmad Gidan Dabino

6. Adamu Muhammad Kwabon Masoyi

7. Abubakar Ishak Zariya

8. Abdullahi Yahaya Mai Zare

9. Bashir Sanda Gusau

10. Balaraba Ramat Yakubu

11. Bala Muhammad Makosa

12. Nura Abdullahi Azara

13. Ibrahim Muhammad Kofar Nasarawa

14. Abba Bature

15. Nazir Adam Saleh

 

Wasu daga cikin Marubuta Jarumai a Farkon Kafuwar Kannywood

1. Ibrahim Mandawari

2. Aminu Hassan Yakasai (marigayi)

3. Bala Anas Babinlata

4. Dan Azumi Baba Chediyar ‘Yan gurasa

5. Ado Ahmad Gidan Dabino, MON

6. Adamu Muhammad Kwabon Masoyi

7. Abubakar Ishak Zariya

8. Nura Abdullahi Azara

9. Hamisu Bature

 

Mujallun da Suke Bayar da Labarin ’Yan Fim da Marubuta Littattafai

Kamfanin Gidan Dabino Publishers, Kano, su ne suka fara buga mujalla ta farko a jihar Kano mai suna Zamani, wadda take bayar da labaru a kan masu yin wasan kwaikwayo da kuma marubuta, a cikin watan Yuli na shekarar 1994 aka fara buga ta. Wannan mujalla tunanin wasu fitattun marubuta ne masu sha’awar ci gaban harshen Hausa, mutanen da suka gudanar da ita su ne Aliyu Abubakar Aliyu da Bala Anas Babinlata da Dan’azumi Baba Chedyar ’Yangurasa da Balarabe Abdullahi Sani da Farfesa Yusuf Muhammad Adamu da Sunusi Shehu Daneji da marigayi Aminu Hassan Yakasai (Allah ya jikansa) da Bashir Sanda Gusau da kuma Ado Ahmad Gidan Dabino, MON.

Mujallar Tauraruwa ita ce mujalla ta biyu da aka samar a wannan masana’anta, ta fito ne a watan Janairun shekarar 1999, Sunusi Shehu Daneji ne ya kafa ta.

Sai mujallar Fim da ta fito a watan Maris, 1999, wadda Ibrahim Shehe ya kafa.

Ado Ahmad Gidan Dabino, MON- ya kafa mujallat Mumtaz a cikin shekarar 2000.

 

Wasu Daga Cikin Sahun Farko na Marubutan da Aka Juya littattafansu Zuwa Fim a Kannywood

1. Ado Ahmad Gidan Dabino- In Da So Da Kauna

2. Dan’azimi Babba Chediyar ‘Yan Gurasa- Bakandamiyar Rikicin Duniya

3. Aminu Hassan Yakasai-Madubi

4. Ibrahim Mandawari- Aminu Mijin Bose

5. Khalid Musa- Kadaura (Hannun Da Ya Ba Da Kyautar

6. Bala Anas Babinlata- Tsuntsu Mai Wayo

7. Bala Muhammad Makosa -Halimatu ko Jummai

8. Adamu Muhammad -Kwabon Masoyi

9. Yusuf Aliyu Lawan Gwazaye- Cinnaka

10. Sunusi Shehu Daneji- Bankwana da masoyi

11. Abba Bature - Auren Jari

12. Abdul’aziz Sani Madakin Gini- Idaniyar Ruwa

13. Aminuddin L. Abubakar (Ala)- Bakar Aniya

14. Abubakar Ishak - Da Da Kyar Na Sha

15. Kabiru Ibrahim Yakasai – Suda

16. Auwalu Y. Hamza- Gidan Haya

17. Aminu Aliyu Argungu- Haukar Mutum

18. Bashir Sanda Gusau - Babu Maraya Sai Rago

19. Bilkisu Salisu Ahmad Funtuwa - Ki Yarda Da Ni

20. Balaraba Ramat- Alhaki Kwikwiyo

21. Ibrahim Birniwa- Maimunatu

22. Maje Elhajij- Sirrinsu

23. Ibrahim M. K/Nassarawa Soyayya Cikon Rayuwa

24. Muhammad .B. Zakari - Komai Nisan Dare

25. Nazir Adam Saleh -Naira Da Kwabo

26. Zuwaira Isa - Mowar Mata

27. Zilkifilu Mohammed - Su Ma ‘Ya’ya Ne (marigayi)

28. Halima A.D. Aliyu - Muguwar Kishiya

29. Rabi’u Abdullahi Sharfadi-Halak

30. Dalhatu Ibrahim Basawa-Cizon Yatsa

31. Kamilu Tahir-Rabi’a

32. Habibu Hudu Darazau – Zafin Nema

33. Lubabatu Ya’u -Yaya Kenan (Kasko)

34. Ibrahim Mu’azzam Indabawa - Boyayyiyar Gaskiya (Ja’iba)

35. Sadiya Garba Yakasai- Wake Daya (Yana)

36. Fauziyya D. Sulaiman- Rumaisa

37. Nasir Umar Ciromawa-Mata Da Kudi

38. Kabir Yusuf Fagge Anka-Kushewar Badi - Hakkin Miji

 

Gudmmawara da marubuta suka bayar ba ta tsaya nan ba kawai, ta gangaro har ga kafa wasu sababbin kamfanoni sanadiyyar zaman da wasu mutanen suka yi a karkashen wadannan marubuta. Sannan ta haka ne wasu ma suka zama marubuta a wannan masana’anta, wasu suka zama masu shiryawa da bayar da umarni, wasu kuma suka zama jarumai, wato sun raini wasu sun koyawa wasu su ma sun iya.

A shekarar 2003, Ado Ahmad Gidan Dabino, MON da Bashir Mudi Yakasai sun gabatar da takarda mai taken: Matsaloli da Nasarorin Masu Shirya Finafinan Hausa Musamman na Kano, an buga takardar a cikin littafin Hausa Home Videos: Technology, Economy and Society wanda Farfesa Abdalla Uba Adamu da Yusuf Adamu da Umar Faruk Jibrin suka zama editocinsa. Ana iya dubawa don samun Karin bayani da kuma ganin yadda marubuta suka bayar da gagarumar gudummawa wajen samuwar ci gaba da bunkasa da kafuwar wasu kamfanoni a wannan masana’anta ta Kannywood.

Kuma marubutan nan har yanzu wasu daga ciki suna wannan masana’antar ba su gudu ba, ko da sun gudu ma suna dawowa

Ina ga idan aka ce kashi 50 cikin dari na ci gaba da bunkasar da kuma kafuwar wannan masana’anta marubuta ne suka kawo su, ina ga ba a yi kuskure ba. Allah ne masani. Na gode.

 

MANAZARTA

Gidan Dabino, A.A, (1995) Muhimmancin Marubuta a Cikin Al’umma,

Takardar da Aka Gabatar a Bikin Kaddamar da Littafin Karshen Mai Zalunci. Koko, Jihar Kebbi: Makarantar Sakandare.

 

Gidan Dabino, A.A, (1993) Gudummawar Adabin Hausa da Addinin Musulunci, Takardar da Aka Gabatar a Taron Kara wa Juna Sani na Dalibai Musulmi na Babbar Makarantar Sakandaren Dawakin Tofa.

 

Gidan Dabino, A.A, (1992) Tasirin Labaran Soyayya ga Al’umma, Musamman ta Hausawa, An Gabatar da Wannan Takarda a Taron Kara wa Juna Ilimi Mai Taken “Rubutu Don Al’umma’’ Wanda Kungiyar “Writers Forum” ta Gudanar, a Majalisar Matasa ta Fagge, Kano.

 

Buba, Malami, Gidan Dabino, A.A, (2004) Adabi Mai Tafiya: Waiwaye A Kan Fasahar Mai Da Littafi Zuwa Fim. Kano: Gidan Dabino Publishers.

 

Yakasai, B.M., Gidan Dabino, A.A, (2004) Matsaloli Da Nasarorin Masu Shirya Finafinan Hausa Musamman Na Kano. Kano: Gidan Dabino Publishers.

 

Hira da Marubuci Bala Anas Babinlata, 07/06/2020, karfe 7:49 na safe

 

Hira da Marubuci Almustapha Adam Muhammad, 07/06/2020, karfe 9:35 na safe


Tuesday, July 14, 2020

SAKAMAKON GASAR MARUBUTAN HAUSA TA ALIYU MUHAMMED RESEARCH LIBRARY, GUSAU INSTITUTE (GI), KADUNA




SAKAMAKON GASAR MARUBUTAN HAUSA TA ALIYU MUHAMMED RESEARCH LIBRARY, GUSAU INSTITUTE (GI), KADUNA.


Labaran da suka tsallake zagaye na farko

1. YINI SITTIN DA ÆŠAYA
2. GUDUNMAWARMU
3. DAMA SUN FADA
4. SANADIYYA
5. DAN WAYE
6. AIKA AIKA
7. KADDARAR ZAWARCI
8. YAN ZAMANI
9. A DALILIN KWARONA VIRUS
10. KA KI NAKA
11. HALIMATU
12. ILLAR ALMAJIRANCI
13. KANA TAKA ALLAH NA TASA
14. BURGAMI A HAMNUN BERAYE
15. WAYE MAKASHINTA

Labaran da suka tsallake zagayen farko
Daga BMB

ALKAWARINMU na HAFSAT SALISU HAMZA





Sunday, July 12, 2020

WUKAR FAMA na HAJ. HASSANA ABDULLAHI HUNKUYI



TALLA! TALLA!! TALLA!!!
Ina makaranta littafaina? Ina yan sari da masu siyan daddaya? Albishirjnku, WUKAR FAWA zai shiga kasuwa ranar Juma'a 17/7/2020 insha Allahu.DUK MAI SO YA YI MUN MAGANA.
Yammatan Kauyensu kayi ayarin zuwa rafi wanka, daga nan su debo ruwa. A wannan ayari akwai Haire. Sanye take da rigar karen miski mai tsadan gaske, taci kwalliya kamar ba rafi zataje ba, koda yake ance anguwa zasuje da ummanta saita gudu ta biyo kawayenta rafi.
Haire gwanar iya wanka a rafi ne, takan goya yammata biyu a bayanta ta hau kan katon dutse ta sulmiyo cikin rafin sai dai kuji karar ruwa tinjim.
Haire, ta na shirin fadawa ruwa kenan wasu yammatan suka shiga tikar dambe. Kwatsam, saiga Gaje abokiyar hamaiyar Haire ta bayyana da nata zugar kawayen, anan wuri ya sake hargitsewa, yan gaza gani su kayi ta zuga Haire da Gaje har su ka harsala, to amma basu danbace ba.
Wata daga cikin kawayen Gaje ta debo kasa a dukkan hannuwanta, ta zo gaban Haire ta tsaya ta na fadin, "Na lura yau bakya jin yin masifa, kuma Wallahi sai kinyi. Matsoraciya kawai. To inba ga tsoro ba, zabi daya anan. Ga na tsiya gana arziki... "
Bata rufe baki ba, Haire ta kabar da na tsiyar, alamar tsiyar ta ke ji ruwa-ruwa. Ai kuwa take wuri ya koma sansanin danbe. Duk sai yammatan su ka ja tunga suna kallon yadda mata ke ba hammata iska.
Kwatsam! wata wahainiya ta keto ciyayi ta fito. Nan kuma sai kallo ya koma gun wahainiyar, take su ka fara tonon ta, yayinda da take ta rikida kalolin kayansu.
Na karshen kayan da ta rikida, shi ne karan miskin Haire, da haka wahainiyar ta fara sanda zata koma inda ta fito. Kawayen Haire su kayi ta zugata, "Tabdi, wallahi kada ki yarda Haire, wahainiyar nan ta raina ki da yawa, ta rasa kayan wacce zata kwafa ta tafi da shi sai naki? Ba irinki ake takawa a kwana lafiya ba"
Zugar ya sami muhallin zama a zuciyar Haire, don haka a fusace ta sa kafa ta taka wahainiyar...
A Taimaka a taya ni talla!

Friday, July 10, 2020

A DALILIN SON KAI - 2 NA IBRAHIM BIRNIWA



A DALILIN SON KAI - 2 NA IBRAHIM BIRNIWA

Zahra’u da Maryam sun keve a cikin xakin Maryam qarfe huxu da rabi ne na yamma a loakcin.Maryam ta xauko album wanda ya kasance cike da hotunan Faruq ta baiwa Zahra’u domin taga gwarzon nata. Zahra’u ta karvi kundin hotunan tariqa buxewa tana kallon kala-kala hotunan Faruq. Kyakkyawan saurayi, ma’abocin iya saka sutura, gaye wayayye ko a hoton. Ta riqa bin hotunan tana kallon su cikin yabawa yayin da suke ‘yar hira ita da Maryam, duk yawancin hirar akan Faruq. A lokacin da ta gama kallon hoton Zahra’u ta tabbatar ya kwanta mata a rai. Ta rufe album xin.

“Mutumin ina ne?” Ta tambayi Maryam.

“Kano.” Maryam ta ce da ita.

“Gaskiya ya haxu, babu shakka kin yi zave. A ina ku ka haxu da shi?”

“A garin nan.” Maryam ta ce, “Ya zo xaurin auren wnai abokinsa, ni kuma ina daga cikin qawayen amarya,sai mukahaxu wajen hada-hadar bikin, ya ji na kwanta masa a rai tun a lokacin da ya fara gani na, saboda hakabai bar garin nan sai da ya bayyanar da soyayyar sa a gare ni, ni kumana amince da shi. Wannan shi ne watan mu kusan na huxu da shi. Mun haxu da shi a watan da muka gama karatu.”

“Gaskiya ya  yi wallahi. Mene ne sana’ar shi?” Zahra’u ta tambaya.

“Fitar da kaya waje, da kuma shigo da na waje ciki.”

Import and export kenan.”

“Sana’ar sa kenan.”

“Ki ce mai kuxi ne gaskiya.”

“Sosai ma kuwa.” Maryam ta ce “In ki ka ga motocin da yake hawa. Xari biyu da hamsin fa ya bani dan shirya wannan bikin.”

“Dubu xari biyu da hamsin?” Zahra’u ta tambaya baki buxe.

“E, wallahi!” Maryam ta tabbatar mata.

Zahra’u ta jijjiga kai, “Lallai ki ce jarumin naki mai gani ne, Allah dai ya tabbatar mana da alkhairi.”

“Ameen.” Maryam ta ce “Na gode da ki kayaba min shi.”

“Na gode da ki ka nuna min shi nima.” Zahra’u ta ce a ranta.

Sun gabatar da duk wani abu da ya kamata su gabatar da dangane da shirye-shirye a ranar koma Maryam ta yi suna tare da Zahra’u tare suka shirya komai. Zahra’u ta fahimci mahaifiyar Maryam, Hanne tana qaunarta kamar yadda mahaifiyarta Umma Hauwa take qaunar Maryam.

Abin da suka yi na qarshe a ranar kafin su dawo gida da magariba shi ne maganar kujeru waxanda za a zazzauna wajen party baiko sun biya kuxi gaba xaya ba rabin kuxi ba. A gajiye suka shigo gidan liqis.

“Sannunku da dawowa.” Hanne ta ce da su.

“Yauwa sannu Umma. Sunka amsa a tare, sannan suke sassamu wuri suka zazzauna a nan tsakar gidan.

“Wash, gaskiya na wujijjiga.” Zahra’u ta ce, “Wai tun ma kafin a zo mai gaba xaya.”

“Ka ji wai ta wujijjiga.” Maryam ta ce, “Sai ka ce ita kaxai ta yi yawon ba da ni ba.”

“To lallai ne ke ki ji yadda na ji.” Zahra’u ta ce “Kin ji ki,ke da kina ta zumuxi ko gajiya ma ba kya ji.”

Hanne da ke can gindin murhu ta yi dariya “Ni ko har da zance ku zo kukarvi girki tun da kun dawo, ni kuma in huta, amma duk kun cika gida da qorafe-qorafe.”

Suka yi dariya.

“Umma ki ka bamu girki ai kuwa a ci jaga-jaga.” Maryam ta ce.

“Ai har gara ma jaga-jaga.” Zahra’u ta ce, sannan ta miqe “Bari dai ki ga na yi wanka ko na dawo garau.” Ta nufi xakin Maryam domin shirin wanka.

“Yi ki fito nima na yi.” Maryam ta ce yayin da ta bi ta a baya zuwa cikin xakin.

Qarfe takwas da rabi na dare.

Zahra’u da Maryam suna kwance akan qatuwar katifar Maryam suna hira, suna jiran barci ya zo ya kwashe su.Ba su fi minti talatin ba da kammala, cin abincin dare suka kwanta saboda a gajiye suke, sakamakon zirga-zirgar da suka yi.

“Zahra’u ina labarin Sani Magaji ne?” Maryam ta tambaya.

“Ke rabu da wannan.” Zahra’u ta ce, “Bai zo ba, wallahi kwata-kwata bai haxu ba.”

“Kai Zahra’u, ke dai kin fiye ruwanido. Ke kenan kullum ki yi ta xauka kina ajiye wa. Ya kamata ki nutsu fa tun kafin kasuwa ta watse.”

“Wa ya gaya miki wancan kasuwar za ta watse?” Zahra’u ta ce, “Ai wannan kasuwar ko yaushe kasa mata kaya ake.”

“Haka ki ke gani?”

“Ya haka na ke gani, haka ne.”

“To shi kenan.” Maryam ta ce, “Yanzu waye gwanin?”

“Ba ni da wani gwani ni.”

“Ke Zahra’u?”

“Wallahi da gaske, duk masu zuwa wuri na, ni ba su yi min ba.” Zahra’u ta ce.

“Ruwan idon ki dai, amma Sanin nan mene ne laifin sa?” Maryam ta ce.

Zahra’u ta xan juya can ta baiwa Maryam baya, “Ina za ki gane laifinsa ke da ba sanin haxuwar maza ki ka yi ba.”

“Ban san haxuwar maza ba kuma na zavo Faruq?” Maryam ta ce.

“Ya zavo ki dai, ba shi ya ganki ya ce yana so ba?” Zahra’u ta ce.

“To dama ni zan je na ce ina son sa ne. Amma kuma da na amince fa?

To ai dolenki neki amince.Wace ce za ta kasa amsa tayin wannan. Gaye ya kai gaye, amma da yake ke mai son kai ce, kina da kamar Faruq, ni kuma ki ke so ki nuna min cewa ba laifi ba ne idan na amincewa Sani, mutumin da ko sutura bai iya sawa ta yi masa kyau ba. Abokin nan nasa Ibrahim ne ma fa yake xan koya masa gayu. Da ma dai Ibrahim xin ne yake so na, to da sai na amince.”

Maryam ta xan yi dariya.

“To ki sace zuciyar Ibrahim xin mana.”

“Tab, wannan ba shi da wata magana kullum sai ta wata wai ita Shafa’atu ‘yar Gusau.”

“Kin tava zuwa Gusau?” Maryam ta tambaya.

“Kai ban tava zuwa ba.”

“Ba ki ma san wajen ina take ba ko?”

“Na sani mana, ba can take ba wajen Baushi?”

“A’a, me ya haxa Gusau kuma da Baushi?” Daga jihar Sokkwato fa aka cire ta.”

“Haba?”

“Allah.”

Haka suka yi ta hira har barci ya xauke Maryam. Zahra’u ba ta sani ba tana ta magana sai ta ankara Maryam ba ta amsawa.

“Maryam!” Ta kira sunanta.

Shiru, ta tabbatar Maryam ta yi barci, sai ta yi shiru itama, ta lumshe idanuwanta ta faxa kogin tunani. Tunanin faruq, mutumin da ba ta tava ganin sa a zahiri ba sai a hoto. Zuciyarta ta karkata gaba xay zuwa gare shi. Ta matsu Talata ta yi domin ya zo ta ganshi a zahiri. Kwanaki ukun da suka rage Talata ta zo sai take ganin su kamar wasu sati uku. Abin da yake tava ranta shi ne sanin cewa babu yadda za ayi ta ganshi dole sai ranar Talatar nan idan ya zo.

Ta tashi zaune a hankali, sannan ta miqa hannu kan wani xan tebur da ke gefen katifar, da suke kwance ta xauko album xin da ke xauke da hotunan Faruqu. Ta buxe album xin ta  riqa kallon hotunan xaya bayan xaya. A lokacin data gama kallon hotunan sai ta album xin ta rungume a qirjinta, tana mai ina ma ina ma, ina ma da ita suka haxu ba da Maryam ba, ina ma ita yake so ba Maryam ba, ina ma baikonta za a yi gata ba na Maryam ba.

Ta xan juya ta dubi Maryam dake kwance tana barci abin ta.

Barcin  ta ma take saboda babu abin da ya dameta ta mallaki saurayi da ya kwanta min a rai. Ta xan jima tana dubanta. Sannan sai ta xaukie kai ga barin kallonta, sannan ta juya ta maida album xin ta ajiye a wurin da ta xauka.

Ta miqa hannu ta kamo makunnar lantarki ta gado ta kashe wuta, duhu ya gauraye xakin, sannan ta rufe idanuwanta ta gayyato barci. Barcin bai zo ba sai bayan da ta shafe sama da minti goma sha biyar tana tunanin Faruq.

Can cikin dare a cikin barcin ta sai ta yi mafarki ana biki. Kuma tana xaya daga cikin qawayen amarya, sai abokan ango suka zo maganar kuxin zanchen, sai ta ga har da Faruq a cikin su. Ya kura mata idoyana ta kallon ta ita ma tana ta kallonsa. Can sai ya kira ta suka keve su biyu.

‘Ina son ki.’ Ya ce da ita.

‘Ina son ka nima.’ Ta amsa masa.

Sai ta ga ya qyalqyale da dariya. Yana ta dariya sai ta ga ya juye ya koma Sani. Ashe dama ba Faruq ba ne Sani ne. Sani ya juya baya yana ta dariyar jin daxin ta ce tana sonsa.

Sai taji ranta ya vaci ‘Bana son ka, ba na sonka...ba na sonka.’ Ta riqa faxa cikin tsawa.

Sani ya juyo. Yana juyowa sai ta ga Faruq ne, ya daina dariya ya vata rai.

‘Ba kya sona?’ ya ce da ita ‘Shi kenan na gode.’ Ya juya, ya tafi, ya bar ta.

A xan lokacin sai ta ruxe ta rasa yadda za ta yi, sai kuma ta daidaita qwaqwalwarta.

‘Ina sonka....ina son ka....’ ta faxa da qarfi. Ta tabbatar ya ji, amma kuma bai tsaya ba ya ci gaba da tafiyar sa, sai ta bi shi da gudu tana ta faxin ‘Ina son ka....’ina son ka...’ tana gudun sai ta yi tuntube ta faxi. Ta yunkura za ta tashi, sai ta farka daga barcin da take.

Da farko ta xan yi jim anan a kwance, tana qoqarin rarrabewa tsakanin mafarkin da kuma gaske. Ta ja dogon numfashi  bayan da ta fita a mafarki, shiru babu wuta an xauke. Ta ji haushi saboda tana son ta sake kallon hoton Faruq. Duk da haka sai ta juya ta sa hannu amma sai ta bubbuxe album xin, ba ta ganin komai xin kuwa sai duhu, ta rufe album xin  ta rungume shi a qirjinta ta faxa tunanin Faruq.

Rungume da hoton a qirjinta, barci ya sake xauketa.

Qarfe takwas na safe maryam ta farka daga barci, da yake xakin a kulle yake har yanzu hasken qwan lantarki yana da tasiri a xakin. Zahara’u ba ta kashe wuta ba kenan, maryam ta zata. Ta tashi, ta zauna nan akan katifar yayin da ta yaye mayafin da take lulluve dashi. A hankali ta juya, ta dubi Zahara’u dake kwance a gefenta tana barci, ga mafarkinta sai ta ga Zahara’u tana rungume da album xin dake xauke da hotunan Faruq. Ta xan jima tana kallon Zahara’u, a cikin zuciyarta tana jujjuya abin da ta gani, tan son ta fahimci al’amarin irin fahimtar da ya dace mene ne hakan ke nufi? Me ya kai Zahara’u rumgume hotunan Faruq har tayi barci da su a qirjin ta.

Maryam tayi tunanin abubuwa da dama amma ta kasa tsaida tunanin ta a kan wani abu guda xaya. Abin da zuciyarta ke qoqarin saqa mata ba za ta amince da shi ba, ba za ta yarda yadda suke da Zahara’u wani abu makamancin abin da zuciyarta take karkata gare shi zai kasance ba.

Ta sa hannu a hankali ta zare album xin daga qirjin Zahara’u ta ajiye shi a wurin da ta saba ajiyewa, sannan sai ta xan doki kafaxar Zahara’u, ta sake  duka. Zahara’u ta farka a hankali, ta buxe idanuwanta kaxan tana xan yatsina fuska a qoqarinta na baiwa idanuwanta damar karvar hasken da ke gauraye da xakin.

Bayan idanuwanta sun tabbatar da sun amince da hasken sai ta buxe idanuwan natasosai ta dubi Maryam dake zaune a kan katifar a gefenta kana tayi miqa da hamma tare da yin salati.

“Tashi gari ya waye.” Maryam ta ce da ita.

Misalin karfe tara da rabi sun kammala da komai. Maryam ta shigo musu da kayan karin kumallo xaki, suka zauna suna ci suna kuma hirar abubuwan da suka shafe su da ma waxanda ba su shafe su ba kamar yadda qawaye suka saba yi. Can cikin hira bayan Maryam ta yi shawara da zuciyar ta sai ta amince ya kamata ta tuntuvi Zahara’u game da al’amarin da ya fara yi mata barka da asuba bayan ta shin ta daga barci yau.

“Zahara’u zan yi miki tambaya.” Maryam ta ce da Zahara’u.

“Ina sauraronki.” Zahara’u ta ce da ita.

Maryam ta kurvi shayi daga kofin da ke riqe a hannunta ta haxiye, sannan ta dubi Zahara’u.

“Wane matsayi ki ka baiwa Faruq nawa a wajenki?”

“Matsayi?”  Zahara’u ta ce “Wane matsayi kuwa ban da matsayin da ya dace da shi?” Zahara’u ta amsa mata.

“Kamar wane matsayi kenan ki ke zaton ya dace da shi?”Maryam ta tambaya.

“Saurayin qawata mana.” Zahara’u ta ce “Yana da wani matsayi da ya wuce ne? Me ya sa ki ka yi min wannan tambayar?” Ta xauki kofin shayi, ta nufi bakinta da shi.

“Na farka daga barci ne yau sai na gan ki rungume da album xin hotunan Faruq, shi ne nake son na san dalilin faruwar hakan.”

Zahara’u ta fasa kurvar shayin da ta kai bakinta, ta dawo da kofin qasa ta ajiye, zuciyarta na jujjuya abin da Maryam ta faxa cikin gaggawa tana son ta tuna abin da ya faru daren jiya da kuma amsar da ta fi dacewa ta baiwa Maryam.

Yanzu jiya barci ta yi album a qirjinta. Ya aka yi ta fara bada qofar da Maryam za ta fahimci wani abu tun yanzu. Ta dubi Maryam za ta fahimci wani abu tun yanzu. Ta dubi Maryam ta yi ‘yar dariyar qarfin hali.

‘Me ki ke so ki ce?’

‘Me na me ke so na ce, ko kuma me na ke so na ji?’ Maryam ta ce.

‘Kar fa ki yi wani tunani na shirme.’ Zahara’u ta ce.

‘Ba zan yi ba.’ Maryam ta ce ‘Shi ya sa ai na tambaye ki.’

‘Ok. Jiya na yi barci, can sai na yi wani mafarki mai ban tsoro, sai na farka nan da nan ke kuwa a lokacin kina barcin ki. Bayan wannan farkawar sai kuma barci ya qi wuza min. Na kwanta nan kawai idona buxe, cike da gundura. Na jima a haka barci bai zo ba, sai na kuma wuta na xan duba ko zan sami wani littafin karatu amma ban ga komai ba, shi ne sai na xauki album xin ina dubawa, ina gayyatar barci. Ban san lokacin da yayi awon gaba dani ba.

 “Ke da me ki ke zato?”

“Babu komai.” Maryam ta ce, sannan ta kurvi shayi ta ajiye kofi, “Kin san ina ji da shi, ina matuqar qaunar sa, ina kuma matuqar kishin sa.”

“Kina kuma matuqar zargi a kansa.” Zahra’u ta ce.

“Idan haka ne za ki ga laifi na?” Maryam ta tambaye ta, tana kallonta cikin ido.

“Ba zan ga laifin ki ba.” Zahra’u ta ce, “Ba zan ga laifin duk wata qawa da ta zargi qawarta da son saurayinta ba.”

“Za ki ga laifin ita qawar da aka zarga idan ta yi fushi?” Maryam ta tambaye ta.

“In dai tabbas an zarge ta xin.” Zahra’u ta ce. Sannan ta shi tsam daga gaban kayan karin kumallon ta koma bakin katifa ta zauna, sannan ta kwanta da baya akan katifar, yayin da qafafunta ke qasa. Ta yi qoqarin nuna fushi a fuskarta. Ya kamata ta nuna ranta ya vaci don hakan ya raunana zargin da Maryam take a ranta.

Maryam ta bi ta da kallo har ta kwanta xin, sannan ta ja dogon numfashi. Ba ta kyauta ba, ya za ta zargi qawarta qud da qud da son saurayin ta, bayan kuma ta faxi dalilin da ya sa ta same ta rungume da album xin hotunan saurayin nata.

“Ki yi haquri Zahra’u.” Maryam ta ce cikin sanyin rai, “Kin san yadda zuciya take kuma kin san yadda so ya ke. Bai kamata na zargi wani abu ba na sani amma na kasa hana kaina ne ki yi haquri don Allah, na gamsu da bayanin ki.” Ta yi shiru don jin abin da Zahra’u za ta ce, amma shiru ba ta ce komai ba.

“Zahara’u!” Ta kira sunanta.

“Don Allah ki qyale ni.” Zahra’u ta ce.

“Ki yi haquri don Allah don Annabi, I am sorry.”

 “Haba Maryam.” Zahra’u ta ce, “Ya ma za a yi ki yi min haka? Don kawai ke kina son Faruq sai ki xauka kowa ta ganshi za ta so shi, har ki fita a hankalinki ki zarge ni da sonsa, an ce miki Faruq ya yi min ne. Na fa yaba shi don kina sonsa, bai kamata na kushe miki shi ba...”

“Na dai ce ki yi haquri don Allah... Haba Zahra’u, ya wuce don Allah, Allah ya huci zuciyarki.”

Matsala.” Zahra’u ta ce a ranta, “Akwai babbar matsala.”


MAKAHO MAI FITILA

MAKAHO MAI FITILA Wani saurayi yana yawo da dare sai ya hangi wani mutum da fitila. Da suka gamu, ya ga ashe makaho ne. Ya ce, "Kai wa...