Monday, November 15, 2021

MA'ANA DA MISALAN KIRARI A HAUSA

 

KIRARI

Kabiru Yusuf Fagge (anka)

Kirari wani tsararren zance ko magana ce ta hikima da akan shirya musamman don kambama mutum ko al’umma ko wani abu.

A takaice dai, kirari shi ne a yabi mutum da wasu kalmomi wadanda za su zuga shi. Sau da yawa akan yi wa mutum kirari a kai shi wani matsayin da bai kai ya je ba. A kan yi wa mutum kirari galibi ta hanyar siffanta shi da ko giwa, zaki, gobara, aljanu, ko wasu fitattun mutane ko masu mulki da sarakuna da makamantansu.

Abin sha'awa da kirari shi ne yadda mutane ke yi wa kansu kirari su koda kansu da kansu. Irin wadannan mutane masu koda kansu sun hada da magori, 'yan tauri, 'yan kokawa, 'yan farauta da sauransu.

Dangambo (1982) ya ce kirari na iya zama yabon kai kamar yadda 'yan tauri ko 'yan dambe ke yi, ko kuma yabon wani kamar yadda maroka ke yi da sauransu.

Kirari ya kunshi yabo da zuga ne. Cikin irin wannan yabo da zuga ne ake amfani da sarrafa harshe cikin hikima.

Zarruk (1986) kuwa ya ce kirari yana da salo irin na magana-magana, waka-waka. Shi ba waka ba saboda ba a rangwadar murya shi kuwa ba magana kara zube ba saboda kana iya jin wani kari a cikinsa. Amma duk da haka akan samu kirari ya fito a cikin waka.

Ire-iren kirari:

 

1. KIRARIN MUTUM

                                           i.      Dan’adam kuzajje da mugunta

                                         ii.      Dan’adam dan mutuwa jikan rasuwa

                                      iii.      Dan’adam kayan Allah ana tare da kai kana tare da halinka.

                                      iv.      Talaka bawan Allah

 

2. KIRARIN MATA

a)           Mata kun riga bugu kun riga tashi

b)          Hantsi kun leka gidan kowa, ba a leka gidanku ba

c)           Matata iyayengida masu akwai da babu

d)          Mata adon gari.

 

3. KIRARIN GARURUWA

                                           i.      Kano jalla babbar Hausa, yaro ko da mai ka zo an fi ka

                                         ii.      Katsina dakin kara

                                      iii.      Bichi kanwar birni

                                      iv.      Kura ta dan baba

                                         v.      Gwambawa diban fari ba a kwana da ku ba an tashi da ku.

                                      vi.      Lagos cunkus dakin tsummma makarin ki sai na dawo

                                    vii.      Gombe ta doma lahirar masu kudi

                                 viii.      Bauchi naman kai ga kitse ga tauri

                                      ix.      Kaduna birnin gwamna

 

4. KIRARIN JAMI'A

                                           i.      Jami'a iyakar boko

                                         ii.      Jami'a uwar boko

                                      iii.      Jami'a gidan ban kashi

                                      iv.      Jami'a matattarar Farfesa daga ke sai Turai.

 

5. KIRARIN SANA'A

                            i.    Noma na duke tsohon ciniki, kowa ya zo duniya kai ya tarar

                          ii.    Jima romon jaba ga kitse ga wari

                        iii.    Saka ba don ke ba da an tafi tsirara

 

6. KIRARIN DUNIYA

                         i.      Duniya ina za ki da mu

                       ii.      Duniya rumfar kara, idan ka hau da karfi ta rushe

                    iii.      Duniya hayakin taba

                    iv.      Duniya kwallon mangoro, kana tsotsarta tana kubuce maka

                       v.      Duniya mai ido a tsakar ka

                    vi.      Duniya budurwar wawa

                  vii.      Duniya makwantar rikici

               viii.      Duniya ba ta auren rago

                    ix.      Duniya gidan kashe ahu

                       x.      Duniya rawar 'yanmata

                    xi.      Duniya mace da ciki, ba a san abin da za ta haifa ba.

 

KADAN DAGA MISALAN KIRARI

1.     Soja marmari daga nesa

2.     Soja na gwamna ga rawa ga yaki

3.     Soja birgimar hankaka

4.     Moda shirgin banza ko a teku sai an danna

5.     Danwake na jakala cimar kuturu, kowa ya ci dubu zai ci dan mutum

6.     Zawo mai saka manya sauri

7.     Daki ko kana zuba ka fi waje

8.     Titi ba a tsallaka ka sai an waiga

9.     Bature ci-gari ka kwana a daji

10.            Bature, babban mutum da rigar yara

11.            Fullo na Gambo, sha ruwa ka binne rijiya

12.            Kudi, na gwamna masu gidan rana

13.            Barebari, na Shehu Larabawan bidi'a

14.            Huntu ubangijin mai riga

15.            Gamji kashe na rabe jikinka

16.            Gwari 'yar gidan kantoma kida kusa wasa nesa

17.            Giwa bukkar daji

18.            Gajere ba yaro ba

19.            Dogo ka ci a reshe

20.            Amarsu ta ango ba kya laifi ko kin kashe dan masu gida

21.            Garin kwaki ko ka yi taimako an wahala

22.            Sauro lange-lange mai ramar keta, rammme haukata kato, sa mutum ya mari jikinsa, mugu hana barci

23.            Hadari malafar duniya

24.            Jikin bushiya ba a masa wawan damka

25.            Tsakin tama gagara tauna

26.            Mushen kura ya wuce Allah Sarki

27.            Damisa ki sabo

28.            Bushiya kowa ya kwana da ke ya kwana salati

29.            Damisa kin ki kallo biyu 

30. Dan-tsakon jimina gagara daukar shaho.

 

Manazarta

Dan Hausa, A.M. (2021) Hausa Mai Dubun Hikima, Kano, Century Research and Publishing Company, Kano Nigeria.

Gwammaje K.D. (2010) Karin Magana a Kasar Hausa, littafi na 1-3 K.D.G Publisher   Kano.

Junaidu I. da ‘Yar’aduwa T.M (2002) “Harshe da Adabin Hausa a Kammale; Don Manyan Makarantun Sakandire.” Spectrum Books Limited, Ring Road, Ibadan-Nigeria

Muhammad, Y.M. (2005) “Adabin Hausa.” Zaria: Ahmadu Bello Unibersity Press Ltd., Samaru-Zaria

Dangambo A. (1982) Rabe-raben Adabin Hausa da Muhimmacin Ga Rayuwar Hausawa, Triumph KanoNigeria.

Dangambo, A. (1984) “Rabe-raben Adabin Hausa da Muhimmancinsa ga Rayuwar Hausawa.” Madaba’ar Kamfanin ‘Triumph’ Gidan Sa’adu Zungur, Kano.

Danhausa, A.M (2012) “Hausa Mai Dubun Hikima.” Kano: Century Research and Publishing Company, Kano-Nigeria

Yahya I.Y. (1988) Hausa A Rubuce, Tarihin Rubuce-rubuce Cikin Hausa N.N.P.C Zaria

Yahya I.Y. da wasu (1992) Darussan Hausa Don Manyan Makarantun Sakandare Littafi na 1-2 Unibersity press PLC Ibadan

Yahya I.Y. da Dangambo A. (1986) Jagoran Nazarin Harshen Hausa N.N.P.C Zaria

Yunusa, Y. (2000) “Hausa a Dunkule.” Kano: Madaba’ar Jakara Bookshop.

Zarruk R.M da wasu (1986) Sabuwar Hanyar Nazarin Hausa Don Kananan Makarantun Sakandire. Littafi na daya. Unibersity Press L.T.D. Ibadan

 

No comments:

Post a Comment

RANAR HAUSA: ƘUNGIYAR HAUSA TA BUK TA CIRI TUTA

 RANAR HAUSA: ƘUNGIYAR HAUSA TA BUK TA CIRI TUTA Nabila Muhammad Ƙungiyar Hausa ta BUK ƙarƙashin jagorancin Kabiru Yusuf Fagge wanda aka fi ...