Thursday, May 28, 2020

GABATAR DA LITTAFIN RUBUTUN FIM Daga Bala Anas Babinlata






GABATAR DA LITTAFIN RUBUTUN FIM
Daga Bala Anas Babinlata

Barkan mu da Sallah, Allah Ya maimaita mana. Ya kare mu daga dukkan masifu, ya kawo mana karshen annobar data tsayar da al'amuran mu na rayuwa.
Kafin Azumi na nemi shawarwarin ku game da sakin sabon littafina mai take Rubutun Fim, in da aka samu rinjaye na shawarwari akan a yi hakuri a bar shi zuwa bayan sallah, Alhamdu lillahi, ga bayan sallah ta zo, amma dan sauyin da aka samu bai taka kara ya karya ba. A gaskiya zai zama kuskure idan muka ce zamu yi taron fuska da fuska na gabatar da wannan littafi, a taron da zai dauki kimanin mutune 300 a waje daya. Ba a gwamnatance ba ko a lafiyance kuskure ne babba. Saboda haka ne na yi nazari a tsanake game da gabatar da wannan littafi.
Dalilina na yin wannan littafin biyu ne, na farko ina so na bayar da gudunmawa ta ga 'yan uwana marubuta da masu sha'awar son yin rubutu musamman na fim. Na biyu wanda shi ne kashin bayan wallafa littafin. Zan yi bayaninsa a takaice duk da dogon labari ne. Da fatan zaku jure karantawa.
Rubutu shi ne Kashin bayan kowane fim, wannan ne ya sa finafinan da aka yi a baya suka yi tasiri, saboda akwai hannayen marubuta, musamman na littafi a ciki. Idan mutum yana da ja ya dubi gidan talabijin na Arewa24 kusan duk marubutan Drama dinsu 'ya'yanmu ne marubutan littafi. Sanin muhimmanci Marubuta a harkar fim ya sa na rinka janyo marubuta ta hanyar workshops don su bayar da gudunmawar su. Rubutattun Littattafai suna taimaka wa sosai a duniya wajen samar da labaran fim, amma mutuwar kasuwar littafi, ko na ce sauyawar kasuwar daga bookshop zuwa online ta kassara samuwar nagartattun littattafai.
A karshen shekarar da ta gabata (2019) na gano kasuwar littattafan ba mutuwa ta yi ba, makaranta sun rasa in da zasu samu littattafan su saya ne, wala a bookshop ko online. Na gano wannan ne daga tattaunawa da mutane a Facebook. Wannan ne dalilin da ya sa na kafa group a Telegram in da marubuta zasu gana da makaranta, su kuma nemi duk littafin da suke so su saya ta book on demand.
Sai dai in da gizo ke sakar, lokacin da muka kira taron Marubuta an samu halarta, amma sai muka fahimci yawancin Marubutan na Da dana Yanzu sun samu tabuwar tattalin arziki, ta yadda ko tsofaffin littattafan su ba zasu iya bugawa a kwamfuta ba, ba wai maganar dab'i ba. Wannan sai ya sa muka sake tara marubutan a ofis din Professor Yusuf Adamu da tunanin mu hada kudi mu yi kamfanin book on demand da website. A nan Professor ya janyo hankalina da kada a yi ta surutu na kawo Marubuta ofishin sa an yi musu wayo. Duk da mun yi dariya, amma maganar ta tsaya min a rai sosai.
Sai na shiga tunanin ta wacce hanya zan bi na taimaka a kafa wannan kamfani tun da Marubuta na cikin wani yanayi? A wannan gabar ne na karkade wannan littafin nawa Rubutun Fim na kammala shi, da tunanin idan muka tara masoyanmu muka gabatar da shi dan abin da aka samu sai na yi amfani dasu na kafa Hausa novels Foundation da zata samar da website da ofishin yin book on demand da zai amfani duk marubuta.

RANAR GABATAR DA LITTAFIN FIM
Kamar yadda na shirya za a gabatar da littafin nan kafin Azumi aka samu akasi, wanda ya sa aka daga zuwa bayan Sallah, to ga bayan Sallah Allah Ya kawo mu, amma taro fuska da fuska ba zai yiwu ba. Na so mu yi amfani da wannan gabatarwar mu gamu da masoyanmu amma Allah bai yarda ba. Amma duk da haka ba zamu fasa gabatarwar ba.
Za a yi gabatarwar ne online. Abin da muke bukata a wannan gabatarwar shi ne gudunmawa daga Marubuta da Makaranta. Akwai Marubuta Sahun farko da na ware wadanda kowane zai sayi kwafin littafin fiye da daya, ma'ana zai sayi nasa ya kuma dubi wani Marubuci mai karamin karfi ya sai masa. Haka nan sauran marubuta da suke da hali zasu sayi nasu kwafin. Sai Makaranta, su ma tasu gudunmawar ita ce su sayi kwafi na littafin, ma'anar wannan gudunmawar ita ce a karshe mu iya tara kudin yin website da bude ofis da na'urar buga littafi na Book on Demand na kowane littafi Makaranci ke bukata.
Sai dai a yi mana afuwa, don zamu wallafa sunayen duk wadanda suka bayar da gudunmawar su ta hanyar sayen littafin don kada tarihi ya manta da kokarin mutane.
Farashin littafi Naira dubu daya. (Tsurar kudin littafi ne wannan, ban da delivery.) Ga masu bukatar online copy za a iya samunsa a okadabooks.
Za a sanar da Lambar bankin da za a biya kudin a ranar Gabatarwar.
Ranar Gabatarwar ita ce Litinin 8 ga watan June, 2020.
Allah Ya ida mana nufi.
A taimaka a taya ni sharing.
Bala Anas Babinlata


Wednesday, May 27, 2020

BARKA DA SALLAH DAGA MARUBUTA





KUDIN KORONA



KUDIN KORONA
Gajeren Labari
Rubutawa: Kabiru Yusuf Fagge

Na yi sharkaf da gumi, saboda irin yadda tun safe nake ratsa unguwanni da kasuwanni a cikin rana, abin ne ya hadar min goma da ashirin, ga rashin kudi, ga rana, ga shi mutane sun ki siyen maganin beran da nake tallan.
A wannan hali da ake ciki mutane ba ta maganin bera suke yi ba, ta abincin da za su ci suke. Fatan da nake yi in samu wadanda ko tayawa su yi in karyar musu in sami abin da zan ci ni da iyalina.
A kwanar shiga unguwar Fagge, n a ji wasu matasa suna hira, hirar ta ja hankalina na koma gefe na rakube ina sauraronsu.

Tuesday, May 26, 2020

DABARUN RUBUTA GAJEREN LABARI



DABARUN RUBUTA GAJEREN LABARI
Kabiru Yusuf Fagge

-Da yawan marubuta da masana sun bayyana hanyoyi da dabarun rubuta gajeren labari, kowannensu ya kawo irin hangensa, kuma da yawa suna taimakawa marubuta wajen kwarewa ga rubuta gajeren labarin.
-A nan, ni ma na dan leka inda ya kamata, na tattara tunanin wasu masana da marubuta don taimaka wa 'yan'uwa marubuta. A sha karatu lafiya.

Friday, May 15, 2020

Gasar Rubutun Gajerun Labaran Hausa Ta AMINIYA-TRUST 2020




Gasar Rubutun Gajerun Labaran Hausa Ta AMINIYA-TRUST 2020

 


GABATARWA
Hukumar Gudanarwa ta GANDUN KALMOMI tare da haxin gwiwar OPEN
ARTS, Kaduna, na kira ga masu sha’awa zuwa shiga GASAR RUBUTUN GAJERUN LABARAN HAUSA TA AMINIYA-TRUST, TA SHEKARAR 2020.
Wannan sabuwar gasa ce ta rubutun gajeren labarin Hausa ta jaridun AminiyaTrust da ake fatar ta kasance wata kafa ko dama domin bunkasa rubuce-rubucen adabi cikin Hausa da za a dinga gabatarwa kowace shekara, karkashin kulawar GANDULKALMOMI da OPEN ARTS da ke Kaduna.

MAUDU’IN SHIGA GASA
Ba kamar saura gasa da aka saba yi a baya ba, wannan gasa za ta dinga zuwa da maudu’i na musamman da ake so masu shiga gasar su gabatar a cikin labaran nasu. Maudu’in wannan shekara ta 2020 shi ne MATSALOLI MULKIN DIMOKURADIYYA DA DAMBARWAR SIYASA A NIJERIYA.
Saboda haka ya zama dole masu shiga gasar su tunkari wannan batu a
cikin labarin nasu ta irin fuskar da suka ga dama, sai dai ana son labarin ya kasance an tsara shi ne ta fuskar ayyanawa, ba abin da ya faru a zahiri ba ko kuma a fassaro shi daga wani harshe ko wani rubutu na daban ba.

YAWAN KALMOMIN GAJEREN LABARIN
Kowane labari ana son kada ya gaza kalmomi 1,000, kada kuma ya wuce kalmomi 1,500, a kuma kayata shi da ka’idojin rubutun Hausa da salo mai birgewa, a kuma tabbata ba a jefa batsa ko wasu kalamai masu iya tada hayaniya ko tashin-tashina ba.

SU WA ZA SU SHIGA GASAR?
An shirya wannan gasa ne domin matasa, MAZA da MATA daga ko’ina suke a fadin duiya, sai dai dole su kasance ‘yan shekara 18 zuwa 35. Ga wadanda ke sha’awar shiga gasar ta hadin gwiwa, to kada su wuce mutum biyu, maza ko mata ko kuma a cakude.
Idan an kammala gasar, za a buga gajerun labaran da suka yi zarra daga na 1 zuwa a 15 a matsayin littafi don adanawa da kuma sayarwa da rarrabawa domin amfanin al’umma.

INA ZA A TURA GAJEREN LABARIN?
A tura gajeren labarin zuwa ga: wasikunaminiya@dailytrust.com tare da cikakken suna da dan takaitaccen bayanin mai shiga gasar da jawabi game da gajeren labarin da kuma adireshin gida ko ofis da na imel da lambar waya.

YAUSHE ZA A BUDE DA RUFE GASAR?
Za a bude amsar gajerun labarun gasar daga ranar 15 ga Watan MAYU, 2020, a kuma rufe karba daga sha biyun daren ranar 15 ga watan YULI, 2020. Duk gajeren labarin da ya zo bayan wannan lokaci da ranar da aka aje, ba za a bi ta kan sa ba.

WACE AWALAJA ZA A SAMU DAGA SHIGA WANNAN GASA?
Wadanda suka zo na daya da na biyu da na uku ne kawai za su sami garabasar kyauta ta kudi kamar haka:
Na daya, Naira 250,000
Na biyu, Naira 150,000
Na uku, Naira 100,000
Bayan kammala gasar, za a buga gajerun labaran 15 da suka yi zarra a matsayin littafi, za a kuma ba marubutan labaran satifiket da wani kaso (da za a aminta da shi nan gaba) na littattafan kyauta.

JADAWALIN AIWATAR DA GASAR
• Daga 15 ga watan Mayu, 2020 za a bude damar shiga gasar, a kuma rufe karbar gajerun labaran daga 15 ga watan Yuli, 2020.
• Daga ranar 15 ga Watan Yuli 2020, za a fara tantance wadanda suka turo da labaransu, inda za a zabi guda 25 da aka tabbatar sun yi zarra.
• A mataki na biyu, wasu zabbabun masana gajerun labarai za su sake tatancewa su fitar da gajerun labarai 15.
• A cikin watan Agusta, 2020, za a tura wa alkalai 3 da aka zaba da gajeru labaran 15 su tantance na 1 zuwa na 15.
• A farkon watan Satumba 2020, za a bayyana wadanda suka lashe gasar baki daya, wato daga na 1 zuwa a 15.
• A cikin watan Satumba da Oktoba za a tace wadannan gajerun labarai guda 15, a kuma wallafa su a matsayi littafi, a kuma fassara na 1 zuwa na 3 zuwa Ingilishi don watsa wa duniya ta gani.
• A watan Nuwamba, 2020, za a yi hira da wadanda suka lashe gasar, wato na 1 zuwa na 15, da za a buga a cikin jaridun AMINIYA da
TRUST da kuma turakar GANDUN KALMOMI da OPEN ARTS, a Intanet.
• A watan Disamba, 2020 za a yi bikin karramawa da bayar da kyaututtuka ga zaratan wannan gasa, a Kaduna.

RANAR HAUSA: ƘUNGIYAR HAUSA TA BUK TA CIRI TUTA

 RANAR HAUSA: ƘUNGIYAR HAUSA TA BUK TA CIRI TUTA Nabila Muhammad Ƙungiyar Hausa ta BUK ƙarƙashin jagorancin Kabiru Yusuf Fagge wanda aka fi ...