Wednesday, May 15, 2019

DANFILLO MAI KANKARA



DANFILLO MAI KANKARA

Gajeren Labarin Dariya

Danfillo ne ya shigo birni cikin azumin nan, ko'ina ya je sai ya ga ana hada-hadar siye da sayarwar kankara babu kama hannun yaro. Danfillo bai yi kasa a gwiwa ba, ya matsa kusa da wani Bahaushe, ya ce "Hwai Kado, do Allah me aka yi da dutsen ruwa haka naga ana ta siyenta?"

Bahaushen ya dube shi, ya ce "Danfillo kenan, ai kankara ce, mugun tsada take, yanzu ka ganta nan ana siyar da ita Naira dari-dari da an jima za ta iya komawa Naira dari da hamsin ko dari biyu, domin da Naira talatin Naira hamsin ake siyar da ita, kafin ta koma darin."


Danfillo ya koma gefe ya yi shiru yana tunani yana girgiza kai, ya ce "Lallai harkar kasuwanci ta samu, ai wannan kawai sai in sara, ba zan sayar ba sai ta yi kwana biyu."

Haka kuwa aka yi, Danfillo ya yi sauri, ya koma ruga, ya siyar da shanunsa guda biyu, ya hada da kudin da ke hannunsa, ya dawo cikin birni ya rinka bi, yana siye duk kankarar da ya tarar, yana kaiwa masaukinsa yana jibgewa, har ya siyi buhunhunan kankara da yawa iya na kudinsa ya jibge, kana ya zauna yana hutawa.

Ya ce, "Alhamdulillahi, ka ga yanzu zuwa jibi ko gata sai in fito da su in rinka siyarwa Naira dari dari biyar-biyar hankalina kwanshe." Ya yi dariyar mugunta kana ya dora da cewa, "Kado bai san kasuwanci ba, ni zan nuna musu mun san binni."

Washegari, Danfillo shiga masauki don gewayar kankara, tun daga kofa ya ci karo da ruwa malale, sannan ga buhunhunan kankara sun yi lankwam a cikin ruwa, duk kankarar ta zagwanye ta zama ruwa. Ai kuwa Danfillo ya dora hannu a ka, ya dasa ihu, wasu da ke kusa suka matso gare shi, suna tambayar lafiya.

Danfillo ya zayyane musu abin da ya faru, cewar ya siyi dutsen ruwa ta koma ruwa. Mutanen nan suka yi kokarin kecewa da dariya, amma suka gintse, daya daga cikinsu ya ce, "Yo kai Danfillo wa ya gaya maka ana ajiyar kankara?"

Suka fashe da dariya.

(c) Kabiru Yusuf Fagge

 


No comments:

Post a Comment

RANAR HAUSA: ƘUNGIYAR HAUSA TA BUK TA CIRI TUTA

 RANAR HAUSA: ƘUNGIYAR HAUSA TA BUK TA CIRI TUTA Nabila Muhammad Ƙungiyar Hausa ta BUK ƙarƙashin jagorancin Kabiru Yusuf Fagge wanda aka fi ...