Wednesday, May 15, 2019

DANFILLO MAI KANKARA



DANFILLO MAI KANKARA

Gajeren Labarin Dariya

Danfillo ne ya shigo birni cikin azumin nan, ko'ina ya je sai ya ga ana hada-hadar siye da sayarwar kankara babu kama hannun yaro. Danfillo bai yi kasa a gwiwa ba, ya matsa kusa da wani Bahaushe, ya ce "Hwai Kado, do Allah me aka yi da dutsen ruwa haka naga ana ta siyenta?"

Bahaushen ya dube shi, ya ce "Danfillo kenan, ai kankara ce, mugun tsada take, yanzu ka ganta nan ana siyar da ita Naira dari-dari da an jima za ta iya komawa Naira dari da hamsin ko dari biyu, domin da Naira talatin Naira hamsin ake siyar da ita, kafin ta koma darin."

Tuesday, May 14, 2019

DA ME ZAN BIYA ALLAH....? 1

DA ME ZAN BIYA ALLAH?....1
Gajeren Labari
Kabiru Yusuf Fagge

Wani hamshakin attajiri, wanda ya yi shekaru tamanin da daya a raye, watarana rashin lafiya ta same shi, yana fama da ciwon mafitsara, baya samun yin fitsari.
Wane tudu wane gangare, bayan aune-aune da aiki irin na likitoci tare da ba shi magunguna attajiri ya samu sauki, aka yi masa lissafin kudaden asibiti da na magunguna da na aiki, ya sa 'ya'yansa suka cake kudin har da kari saboda jin dadi.

Sunday, May 12, 2019

Gajeren Labari: ROMON DIMOKRADIYYA


ROMON DIMOKRADIYYA
Kabiru Yusuf Fagge

Muna tafe, tafiya mai nisa, kuma mai wahala, duk da motar da muke ciki akwai na'urar sanyaya wuri da kuma tausasan kujeru da nutsuwa, amma a hakan duk na jigata saboda rashin kyan hanya ga kuma zafin rana.
Cikin damuwa, na dubi Cif Kamfen na ce masa, "Wai shi ma wannan garin da za mu je, duk a cikin jihar Natsira yake?"
Cif Kamfen ya yi dariyar yake, shi ma dai kallona yake yi, ya ce "Honorabil ka manta ne, wancan karon fes tenuwa ai mun zo, garin Kumaji ne fa, ka tuna da muka zo, har muka yi musu alkawaruka, wadanda sun fi damuwa da batun ruwan sha..."
Na yi shiru ina tunani, can dai na tuna din, "Gaskiya kam, sai yanzu na tuna, ni tuni ma na manta da su da dukkan alkawuran da muka yi musu a wancan lokacin kafin mu ci zabe..."
"Kuma ka ga kamar yadda ka ce ka manta da garin, haka ma mun manta ba mu cika musu alkawarukan da muka daukar musu ba." Cewar Cif Kamfen.
Na girgiza kai, "Kwarai kuwa, ai abin ne da yawa, gari kamar Natsira ba karamin gari ba."
Cif Kamfen ya dube ni, "To yanzu dai ga shi mun dawo gare su da wata bukatar ya kake ganin za a yi?"
Na yi murmushi, "Idan ka dubi wahalar tafiyar nan da hanyar nan, ka san da wuya a samu masu ilimi a garin nan, bare kuma wayayyu, kawai muna zuwa zan sake yi musu wani alkawarin, don su sake zabarmu, daga baya idan mun tuna da su sai mu yi musu rijiyoyin burtsatse ko guda biyu ne, idan kuma mun manta shi kenan, ai ba su kadai ba ne mutanen jihar nan ba." Na kammala maganar tawa ina wage baki cikin yake, a raina Allah-Allah nake mu je garin mu yi abin da zamu yi, mu baro su.
Na lura da irin kallon da Cif Kamfen yake yi min, a zahiri yana so ya gaya min abin da na fada ba daidai ba ne, amma kawai ya yi min shiru. Kuma ni da shi mun san abin da muke yi zalunci ne, amma mun take gaskiya.

RANAR HAUSA: ƘUNGIYAR HAUSA TA BUK TA CIRI TUTA

 RANAR HAUSA: ƘUNGIYAR HAUSA TA BUK TA CIRI TUTA Nabila Muhammad Ƙungiyar Hausa ta BUK ƙarƙashin jagorancin Kabiru Yusuf Fagge wanda aka fi ...