Thursday, May 30, 2024

SABON ƊAN ISKA

 SABON ƊAN ISKA

Ƙarfe biyar da ‘yan mintuna na yammacin ranar Asabar na ƙaraso ƙofar gidan galar, a lokacin samari ‘yan bana-bakwai da manyan banza ‘yan bariki, haɗi da tarin ƙananan ‘yanmata masu ƙananun shekaru, jingim a wajen, wasu a tsattsaye a ƙofar gidan, wasu kuma suna shiga ciki.

Ni ma, na bi layin shiga ina kallo da nazarin al’ummar da ke wurin, musamman ƙananan ‘yanmatan da suke a matsayin karuwai. Da yawan yaran suna da siffar mutanen kirki, wasu siffofin ababen tausayi, haka nan akwai masu siffar dolaye, kai wasu ma za ka iya rantsewa idan aka saka musu hannu a baki ba za su cije ka ba, amma Alƙur’an idan ka biye musu sai su tsunduma ka a jahannama.

A haka muka ƙarasa bakin ƙofar na biya, na shiga. Yanayin cikin gidan irin na gala ne, kujeru ne da bencina a wani makaken fili sun zagaye dandamali. A cakuɗe ake maza da matan, wasu ma yaran matan a kan mazajensu suke a zazzaune suna ta shafa tare da lala iskancinsu.

Akwai DJ mai sako kiɗoɗi a gefe, ban ga ɓangaren ‘yan rawa ba sai na fuskanci a kan iya ba duk ja’irar da take so dama ta fita kan dandamali, ta cashe, ‘yan liƙi su yi mata liƙi.

Can gefe na koma, na zauna don in nazarci wurin a tsanake. Ina zama wani ƙaton farin mutum ya nufo inda nake, kafin ya iso na tuno tun a waje yake yi min kallon rashin yarda. Na haɗiyi yawu, ya ƙaraso, ya zauna dab da ni yana fuskantata har numfashinsa na karo da nawa, ya zuban jajayen na mujiyarsa.

“Sunana Uban Rabaje. Wane ne kai?” Ya tambaye ni.

“Kamar yaya?”

“Saboda ban yarda da kai ba.”

“Me ya sa?”

“Ban taɓa ganin ka a gidan nan ko sauran gidajen gala ba, sannan da ka shigo, ka dawo nan gefe ka rakuɓe, abu na uku ko irin ‘yar sigarin nan ba ka sha bare in gan ka da wata cika kuna holewa.”

“Ka sani ko ni sabon zuwa ne.”

“Ko sabon zuwan ne, ban yarda da kai ba, ka gaya min gaskiya, me ka shigo yi, kuma wane ne kai?”

“Ni sabon ɗan iska ne.”

Ya harare ni, “Kar ka yi min ƙarya, ni ɗin nan da kake gani, sunana Uban Rabaje na ƙyanƙyashe sabbin ‘yan iska sun fi dubu maitan, idan na ga sabon shiga ina ganewa.”

A lokacin aka fara shagalin galar, yaran matan ke fitowa su rinƙa bin kiɗan da waƙar da ake yi da rawar tamɓele, tare da haɗuwar jiki da samarinsu, waɗanda aka burge sukan yi liƙi, wasu kuma su yi shewa.

Sha’anin shargalle a gidan nan ba sai na siffanta a nan ba, saboda tsaro. Uban Rabaje ne ya karkato da hankalina gare shi.

“In gaya maka gaskiya, ko kai ɗan iska ne ko ɗan hisba ko soja ne ba ka isa ka yi komai ba. Duk fitar da ‘yan hisba ke yi ba sa iya zuwa nan su hana mu aikinmu ba . ‘Yansanda kai ko kwamishina bai isa ya yi kame a gidan nan ba.”

“Saboda me?” Na tambaye shi.

Ya harare ni, “Kar ka raina min waye, na tambaye ka wane ne kai ba ka ba ni amsa ba, kana tambaya ta.”

“Ai na gaya maka, ni sabon  ɗan iska ne.”

Ya ƙara matso ni, yana huci kamar a cikin hancina, ya ƙwalolo min idanu har sai da na ji dam.

“Wane ne kai na ce?”

“Ni marubuci ne.”

“Me ya kawo ka?”

“Harkar rubutu, yadda kuke haɗa ƙananan ‘yanmata da samari kuna casu ba tare da Hisba ko hukuma ta hana ku ba, shi ya sa na ga ina da abin rubutawa da zan yaɗa wa duniya ta karanta.”

“Da kyau, tun da a iya rubutu ka tsaya. Ka ji dai na gaya maka hisba ko ‘yansada ma ba za su iya yi mana komai ba bare rubutunka da a yanzu mutane ma ba karantawa suke yi ba, in ma sun karanta a matsayin tatsuniya za su ɗauka.”

Kallon shi kawai nake yi.

“Kai yanzu har sai ka shigo ka ga ƙwaƙwaf?”

“E mana, ta haka zan rubuta zahiri.”

“To in haka ne, zan iya taimaka maka?”

“Da me?”

“Zan iya haɗa ka da wata sokuwar ƙaramar yarinya wadda tun a nan za ta iya saka kuka.”

“Saboda daɗi ko wuya?”

“Saboda da daɗi mana, yadda za ka ji daɗin yin rubutun.”

Na girgiza kai, “a’a.”

“To a yi maka shokin mana.”

“A’a.”

“Anya kana son rubutu yadda harkar take sosai kuwa?”

“E mana, ai a haka ma zan yi ginin da tunani irin namu na marubuta yadda za a karanta abin kamar yadda yake.”

Ya girgiza kai, “Ba ka isa ba, dole sai  ka yi a zahiri, ai na san darajar rubutu ni ma.”

Ya tashi, ya nufi can wani ɓangare na gidan, ina hango shi ya tattaro wasu yara ‘yanmata masu siffar ƙwallaye sa ƙartai kuka, ya nufo inda nake, suna zuwa ya tarar ba na nan yana ta dube-dube, ina can ɓoye ƙarƙashin wani tebur ina hango shi.

Yana juya baya na nufi bakin ƙofar fita ya hango ni, “Kai marubuci ina kuma za ka je?”

Na ɗaga masa hannu, “Ina dawowa,” na fice. Kuma fa zan koma, amma neman labari.

Rubutawa: Kabiru Yusuf Fagge (anka)

Tuesday, May 21, 2024

BAYAN TA FASHE

 *BAYAN TA FASHE*

(gajeren labari)


Ɗanbashir na tsaye shi da Jummala suna zance, mahaifin Jummalar mai suna Malam Iliya ya ƙaraso, yana kallonsu.

“Ke Jummala na san ba ki gaya masa saƙona ba, shi ya sa na zo da kaina.”

Cikin saddar da kai Jummala ta ce, “Yanzu zan gaya masa Baba...”

Ya dakatar da ita, “Ai tun da na zo an gama.” Ya karkata ga Ɗanbashir, “Kai ya maganar da muka yi game da tsayar da ranar ɗaurin aure, mun gaji da ganinta a gida, kuma kai, ka ƙi ka turo mu tsayar da ranar.”

Cikin ladabi Ɗanbashir ya amsa da cewa, “E wallahi Baba, na gaya mata ina jiran mining ɗin da nake yi ta fashe ne zuwa ƙarshen watan nan sai in ƙarasa  kayan lefen da ginina sai a ɗaura auren.”

Malam Iliya ya sauya masa kallo, “Abin ya zo, in ji mijin karuwa, ashe kai ma kana cikin ire-iren mahaukatan yaran da ake yayi a wannan zamani, masu hauka da tunanin suna neman kuɗi.”

“Baba ba hauka ba ne, nema ne..”

“Nema wanne iri? Kai ban da ka samu taɓuwar ƙwaƙwalwa kawai don kana daddana tare da shasshafa fuskar waya sai a ɗauki kuɗi a ba ka, ba tare da aikin fari ba?”

“Baba wannan daddanawar da shasshafawar su ne aikin.”

“Aiki? A garin gaɓa-gaɓa ko?”

“A’a a duniyar cigaba da masu hankali.”

“Wai ta yaya?”

“Yauwa Baba kamar dai yadda kake zuwa aiki kasuwar Singa, ka sauke kaya, ke jera, ka yi lissafi, ka bayar da yamma a biya ka, haka muke yin namu aikin a ƙarshe a biya mu.”

“Kai, kar ka raina min hankali mana. Ni da nake biyan kudin mota, na je kasuwar, na ɗauki kayan a wuyana ko a kaina, in sauke in shigar a shago, ina gumi, shi ne za ka haɗa ni da kai mai halin ci-ma-zaune?”

“Baba zamani ne ya zo da yanayin haɗa sana’o’i kamar biyu zuwa uku, ka san ni tela ne, nake haɗawa da mining ɗin kuma aiki nake kamar yadda kake yi sai dai a zamanance.”

“Kai ɗan zamani saurara, na daɗe a duniyar nan kafin kai, kuma ga ni a zamanin bare ka layance min, don haka daga yau ba kai ba Jummala, ba zan miƙa ta ga mai matacciyar zuciya ba,” Ya kalli Jummala wacce ke tsaye cikin damuwa, ya daka mata tsawa, “Wuce gida, kin yi min ƙuri kamar tsohuwar mayya.”

Jummala ta nufi gida tana kuka. Ɗanbashir ya marairaice, “Don Allah Baba kar ka raba ni da Jummala, wallahi ina son ta, tana fashewa zan...”

Ya kuza masa tsawa, “Ɓace min da gani kar in yi buju-buju da kai, ka je can ta fashe maka.”

Cikin damuwa Ɗanbashir ya tafi kamar zai yi kuka.

Kwanaki tara tsakani aka ɗaura auren Jummale da wani Ɗankarota. Dole Ɗanbashir ya haƙura, kuma kuɗin da yake tsammanin zuwansu na mining ba su zo ba a ƙarshen watan, sai bayan kwanaki ashirin da shida, inda ya sami manyan kuɗaɗen da shi kansa bai zata ba.

Da yake ya tsara, sai ya kammala ginin gidansa, sannan ya ƙara jari a sana’arsa ta ɗinki inda ya haɗa har da buɗe sabon shagon sayar da atamfofi da lesuna, kuma ya sayi sabuwar mota.

A lokacin kyawawan ‘yanmata da suka ninka Jummala kyau sau ɗari da goma sha uku suka rinƙa tururuwa gare shi, suna son shi da aure.

Sai da ya zaɓa, ya sami mai son shi don Allah ya darje, wata yarinya mai suna Zahra, ya aura.


-Kabiru Yusuf Fagge (anka)

2024

RANAR HAUSA: ƘUNGIYAR HAUSA TA BUK TA CIRI TUTA

 RANAR HAUSA: ƘUNGIYAR HAUSA TA BUK TA CIRI TUTA Nabila Muhammad Ƙungiyar Hausa ta BUK ƙarƙashin jagorancin Kabiru Yusuf Fagge wanda aka fi ...