Saturday, March 1, 2025
Tuesday, February 18, 2025
TARIHIN GASAR GUSAU INSTITUTE A TAƘAICE
Gasar Gusau Institute
Daga Hassana Sulaiman Matazu
Gasar Gusau wata gasa ce da aka samar a tsakanin marubuta, ake kuma gudanar da ita duk shekara ta hanyar zaɓar mutane uku da suka fi cancanta domin ba su shaidar girmamawa da kuma ɗan abin da zai ƙara musu ƙarfin guiwa a karsashin rubutu. Bayan mutane uku akan ware mutane goma a ba su shaidar girmamawa (certificate).
Waye Yake Ɗaukar Nauyin Gasar?
Mai girma General Aliyu Muhammad Gusau shi ne ya asasar da yin gasar tare da wasu magoya baya da suke aiki ƙarƙashin ɗakin karatunsa dake jihar Kaduna wato Gusau Institute.
Dalilin Kafa Gasar
An samar da gasar ne domin tabbatar da kawo ci gaban rubutu da marubuta ta fuskar kawo wata gasa da za ta kawo goggaya domin bayyana baiwar da kowa ne marubuci yake da ita a fagen rubutu.
Bambancin Gasar Gusau
Abubuwa da yawa sun bambanta gasar Gusau da sauran gasanni, wanda har wasu da yawa suke ganin cewar gasar Gusau ta fi ta BBC Hikayata. Domin ita gasar BBC labari ne gajere, kuma kalmomi kaɗan. Idan rabo da sa'a suka yi tasiri wanda bai taɓa cin gasa ba ma zai iya cin BBC Hikayata. Hakan ya faru sau ba adadi.
Dalilin haka ne da yawa suka yarda cewa, gasar Gusau sai jajjirtacen marubuci kuma mai bincike yayin gudanar da rubutunsa tare da tsantsar hikima ne yake iya haye matakan gasar. Kuma ba irin sauran gassanni ba ce masu ɗauke da kalmomi kaɗan da za ka je wani ya rubuta maka ka haye kamar yadda wasu suke yi.
Gwaraza da Labaran Gusau Daga 2018-2024
Shekarar 2018
Bello Hamisu Ida 1st
SABO DA MAZA
Danladi Haruna 2nd
ƁARAYIN ZAMANI
Nura Sada Nasimat 3rd
INUWAR WANI
Shekarar 2019
Abdullahi Hassan Yarima 1st
TAMANIN DA TARA
Zaharaddin Kalla 2nd
MURUCIN KAN DUTSE
Ado Abubakar Bala 3rd
HUSUFIN FARIN CIKI
Shekarar 2020
Jibrin Adamu Rano 1st
DA MA SUN FAƊA MIN
Lantana Ja'afar 2nd
ILLAR ALMAJIRANCI
Zulahat Sani Kagara 3rd
ƊAN WAYE?
Shekarar 2021
Hassana Suleiman Isma'il Matazu 1st
FITSARIN FAKO
Ibrahim Yahaya Shehu 2nd
ƁADDABAMI
Mubarak Idris Abubakar 3rd
RUMFAR KARA
Shekarar 2022
Bilkisu Muhammad Garkuwa 1st.
ƘADDARAR RAYUWA
Hajara Ahmad Maidoya 2nd.
ƊANYEN KASKO
Muttaƙa A Hasaan 3rd.
ƊAUKAR JINKA
Shekarar 2023
Hauwa Shehu 1st
HARIN GAJIMARE
Ruƙayya Ibrahim 2nd
WATA DUNIYA
Fatima Sani 3rd
AMANATUN AMANA.
Shekarar 2024
Rufa'i Abubakar Adam 1st
MARUBUCIYA
Ummi Abba Muhammad 2nd
ABINDA KA SHUKA
Zainab Abdullahi 3rd
WASA DA RAYUWA
Jigunan Labaran 2018-2024
2018
1-Boko Haram
2-Cyber Security
3-Safara
2019
1-Jarida (Investigation)
2-
3-Gajerun Labarai
2020
1-Aljanu/Mafiya
2-Illar Almajiranci
3-Rashin Ilmi
2021
1-Garkuwa Da Mutane
2-Tsaro/Kishin ƙasa
3-Rikicin Ƙabilanci
2022
1-Mata Maza/Zabiya
2-Mata Maza
3-Rikicin Ƙabilanci
2023
1-Cyber Security
2-Sama Jannati
3-Fyaɗe
2024
1-Bincike/Rubutu
2-Kwaɗayi Son Zuciya
3-Matsalar Tsaro
Rubutawa Hassana Sulaiman Matazu.
Wednesday, August 28, 2024
RANAR HAUSA: ƘUNGIYAR HAUSA TA BUK TA CIRI TUTA
RANAR HAUSA: ƘUNGIYAR HAUSA TA BUK TA CIRI TUTA
Nabila Muhammad
Ƙungiyar Hausa ta BUK ƙarƙashin jagorancin Kabiru Yusuf Fagge wanda aka fi sani da Kabiru Anka ta ciri tuta a yayin gudanar da wata 'yar ƙwarya-ƙwaryar gasa ta bajekolin al'adun Hausawa a taron.
Ƙungiyar ta zama ta farko a cikin jerin ƙungiyoyin makarantun gaba da sakandire da ta fara nuna bajinta wajen bayyana zuri'ar Bahaushe ta hanyar sanya ire-iren sutturun da Hausawan ke sanyawa da kuma alamunsu har ma da irin karin harshen da suke amfani da su.
Wasu daga cikin makarantun da suka baje hajar fasahohinsu sun haɗar da FCE da jani'ar Yusuf Maitama Sule da sauransu.
Taron ya samu halartar manyan Farfesoshi da Daktoci na makarantu daban-daban tare da masu fasahohin baka da mawaƙa irin su Aminu Ladan Abubakar Alan Waka da tarin 'yan jarida da sauransu.
An gudanar da taron a ranar 26 ga wannan wata na Agusta, 2024 a ɗakin taro na makarantar YUMSUK da ke Ƙofar Nassarawa.
Thursday, May 30, 2024
SABON ƊAN ISKA
SABON ƊAN ISKA
Ƙarfe biyar da ‘yan mintuna na yammacin ranar Asabar na ƙaraso ƙofar gidan galar, a lokacin samari ‘yan bana-bakwai da manyan banza ‘yan bariki, haɗi da tarin ƙananan ‘yanmata masu ƙananun shekaru, jingim a wajen, wasu a tsattsaye a ƙofar gidan, wasu kuma suna shiga ciki.
Ni ma, na bi layin shiga ina kallo da nazarin al’ummar da ke wurin, musamman ƙananan ‘yanmatan da suke a matsayin karuwai. Da yawan yaran suna da siffar mutanen kirki, wasu siffofin ababen tausayi, haka nan akwai masu siffar dolaye, kai wasu ma za ka iya rantsewa idan aka saka musu hannu a baki ba za su cije ka ba, amma Alƙur’an idan ka biye musu sai su tsunduma ka a jahannama.
A haka muka ƙarasa bakin ƙofar na biya, na shiga. Yanayin cikin gidan irin na gala ne, kujeru ne da bencina a wani makaken fili sun zagaye dandamali. A cakuɗe ake maza da matan, wasu ma yaran matan a kan mazajensu suke a zazzaune suna ta shafa tare da lala iskancinsu.
Akwai DJ mai sako kiɗoɗi a gefe, ban ga ɓangaren ‘yan rawa ba sai na fuskanci a kan iya ba duk ja’irar da take so dama ta fita kan dandamali, ta cashe, ‘yan liƙi su yi mata liƙi.
Can gefe na koma, na zauna don in nazarci wurin a tsanake. Ina zama wani ƙaton farin mutum ya nufo inda nake, kafin ya iso na tuno tun a waje yake yi min kallon rashin yarda. Na haɗiyi yawu, ya ƙaraso, ya zauna dab da ni yana fuskantata har numfashinsa na karo da nawa, ya zuban jajayen na mujiyarsa.
“Sunana Uban Rabaje. Wane ne kai?” Ya tambaye ni.
“Kamar yaya?”
“Saboda ban yarda da kai ba.”
“Me ya sa?”
“Ban taɓa ganin ka a gidan nan ko sauran gidajen gala ba, sannan da ka shigo, ka dawo nan gefe ka rakuɓe, abu na uku ko irin ‘yar sigarin nan ba ka sha bare in gan ka da wata cika kuna holewa.”
“Ka sani ko ni sabon zuwa ne.”
“Ko sabon zuwan ne, ban yarda da kai ba, ka gaya min gaskiya, me ka shigo yi, kuma wane ne kai?”
“Ni sabon ɗan iska ne.”
Ya harare ni, “Kar ka yi min ƙarya, ni ɗin nan da kake gani, sunana Uban Rabaje na ƙyanƙyashe sabbin ‘yan iska sun fi dubu maitan, idan na ga sabon shiga ina ganewa.”
A lokacin aka fara shagalin galar, yaran matan ke fitowa su rinƙa bin kiɗan da waƙar da ake yi da rawar tamɓele, tare da haɗuwar jiki da samarinsu, waɗanda aka burge sukan yi liƙi, wasu kuma su yi shewa.
Sha’anin shargalle a gidan nan ba sai na siffanta a nan ba, saboda tsaro. Uban Rabaje ne ya karkato da hankalina gare shi.
“In gaya maka gaskiya, ko kai ɗan iska ne ko ɗan hisba ko soja ne ba ka isa ka yi komai ba. Duk fitar da ‘yan hisba ke yi ba sa iya zuwa nan su hana mu aikinmu ba . ‘Yansanda kai ko kwamishina bai isa ya yi kame a gidan nan ba.”
“Saboda me?” Na tambaye shi.
Ya harare ni, “Kar ka raina min waye, na tambaye ka wane ne kai ba ka ba ni amsa ba, kana tambaya ta.”
“Ai na gaya maka, ni sabon ɗan iska ne.”
Ya ƙara matso ni, yana huci kamar a cikin hancina, ya ƙwalolo min idanu har sai da na ji dam.
“Wane ne kai na ce?”
“Ni marubuci ne.”
“Me ya kawo ka?”
“Harkar rubutu, yadda kuke haɗa ƙananan ‘yanmata da samari kuna casu ba tare da Hisba ko hukuma ta hana ku ba, shi ya sa na ga ina da abin rubutawa da zan yaɗa wa duniya ta karanta.”
“Da kyau, tun da a iya rubutu ka tsaya. Ka ji dai na gaya maka hisba ko ‘yansada ma ba za su iya yi mana komai ba bare rubutunka da a yanzu mutane ma ba karantawa suke yi ba, in ma sun karanta a matsayin tatsuniya za su ɗauka.”
Kallon shi kawai nake yi.
“Kai yanzu har sai ka shigo ka ga ƙwaƙwaf?”
“E mana, ta haka zan rubuta zahiri.”
“To in haka ne, zan iya taimaka maka?”
“Da me?”
“Zan iya haɗa ka da wata sokuwar ƙaramar yarinya wadda tun a nan za ta iya saka kuka.”
“Saboda daɗi ko wuya?”
“Saboda da daɗi mana, yadda za ka ji daɗin yin rubutun.”
Na girgiza kai, “a’a.”
“To a yi maka shokin mana.”
“A’a.”
“Anya kana son rubutu yadda harkar take sosai kuwa?”
“E mana, ai a haka ma zan yi ginin da tunani irin namu na marubuta yadda za a karanta abin kamar yadda yake.”
Ya girgiza kai, “Ba ka isa ba, dole sai ka yi a zahiri, ai na san darajar rubutu ni ma.”
Ya tashi, ya nufi can wani ɓangare na gidan, ina hango shi ya tattaro wasu yara ‘yanmata masu siffar ƙwallaye sa ƙartai kuka, ya nufo inda nake, suna zuwa ya tarar ba na nan yana ta dube-dube, ina can ɓoye ƙarƙashin wani tebur ina hango shi.
Yana juya baya na nufi bakin ƙofar fita ya hango ni, “Kai marubuci ina kuma za ka je?”
Na ɗaga masa hannu, “Ina dawowa,” na fice. Kuma fa zan koma, amma neman labari.
Rubutawa: Kabiru Yusuf Fagge (anka)
Tuesday, May 21, 2024
BAYAN TA FASHE
*BAYAN TA FASHE*
(gajeren labari)
Ɗanbashir na tsaye shi da Jummala suna zance, mahaifin Jummalar mai suna Malam Iliya ya ƙaraso, yana kallonsu.
“Ke Jummala na san ba ki gaya masa saƙona ba, shi ya sa na zo da kaina.”
Cikin saddar da kai Jummala ta ce, “Yanzu zan gaya masa Baba...”
Ya dakatar da ita, “Ai tun da na zo an gama.” Ya karkata ga Ɗanbashir, “Kai ya maganar da muka yi game da tsayar da ranar ɗaurin aure, mun gaji da ganinta a gida, kuma kai, ka ƙi ka turo mu tsayar da ranar.”
Cikin ladabi Ɗanbashir ya amsa da cewa, “E wallahi Baba, na gaya mata ina jiran mining ɗin da nake yi ta fashe ne zuwa ƙarshen watan nan sai in ƙarasa kayan lefen da ginina sai a ɗaura auren.”
Malam Iliya ya sauya masa kallo, “Abin ya zo, in ji mijin karuwa, ashe kai ma kana cikin ire-iren mahaukatan yaran da ake yayi a wannan zamani, masu hauka da tunanin suna neman kuɗi.”
“Baba ba hauka ba ne, nema ne..”
“Nema wanne iri? Kai ban da ka samu taɓuwar ƙwaƙwalwa kawai don kana daddana tare da shasshafa fuskar waya sai a ɗauki kuɗi a ba ka, ba tare da aikin fari ba?”
“Baba wannan daddanawar da shasshafawar su ne aikin.”
“Aiki? A garin gaɓa-gaɓa ko?”
“A’a a duniyar cigaba da masu hankali.”
“Wai ta yaya?”
“Yauwa Baba kamar dai yadda kake zuwa aiki kasuwar Singa, ka sauke kaya, ke jera, ka yi lissafi, ka bayar da yamma a biya ka, haka muke yin namu aikin a ƙarshe a biya mu.”
“Kai, kar ka raina min hankali mana. Ni da nake biyan kudin mota, na je kasuwar, na ɗauki kayan a wuyana ko a kaina, in sauke in shigar a shago, ina gumi, shi ne za ka haɗa ni da kai mai halin ci-ma-zaune?”
“Baba zamani ne ya zo da yanayin haɗa sana’o’i kamar biyu zuwa uku, ka san ni tela ne, nake haɗawa da mining ɗin kuma aiki nake kamar yadda kake yi sai dai a zamanance.”
“Kai ɗan zamani saurara, na daɗe a duniyar nan kafin kai, kuma ga ni a zamanin bare ka layance min, don haka daga yau ba kai ba Jummala, ba zan miƙa ta ga mai matacciyar zuciya ba,” Ya kalli Jummala wacce ke tsaye cikin damuwa, ya daka mata tsawa, “Wuce gida, kin yi min ƙuri kamar tsohuwar mayya.”
Jummala ta nufi gida tana kuka. Ɗanbashir ya marairaice, “Don Allah Baba kar ka raba ni da Jummala, wallahi ina son ta, tana fashewa zan...”
Ya kuza masa tsawa, “Ɓace min da gani kar in yi buju-buju da kai, ka je can ta fashe maka.”
Cikin damuwa Ɗanbashir ya tafi kamar zai yi kuka.
Kwanaki tara tsakani aka ɗaura auren Jummale da wani Ɗankarota. Dole Ɗanbashir ya haƙura, kuma kuɗin da yake tsammanin zuwansu na mining ba su zo ba a ƙarshen watan, sai bayan kwanaki ashirin da shida, inda ya sami manyan kuɗaɗen da shi kansa bai zata ba.
Da yake ya tsara, sai ya kammala ginin gidansa, sannan ya ƙara jari a sana’arsa ta ɗinki inda ya haɗa har da buɗe sabon shagon sayar da atamfofi da lesuna, kuma ya sayi sabuwar mota.
A lokacin kyawawan ‘yanmata da suka ninka Jummala kyau sau ɗari da goma sha uku suka rinƙa tururuwa gare shi, suna son shi da aure.
Sai da ya zaɓa, ya sami mai son shi don Allah ya darje, wata yarinya mai suna Zahra, ya aura.
-Kabiru Yusuf Fagge (anka)
2024
Friday, April 5, 2024
Wednesday, November 8, 2023
KAWALCI A ƘASAR HAUSA
KAWALCI A ƘASAR HAUSA
Kabiru Yusuf Fagge (Anka)
Kawalci yana ɗaya daga cikin munana ɗabi’u da suka zama
ruwan dare ba kawai a ƙasar Hausa ba har ma a duniya bakiɗaya.
Kawalci shi ne ɗabi’ar haɗa namiji da mace ko namiji da namiji
ko ma mace da mace don su yi aikin assha, inda yawanci mai haɗawar wato “Kawali”
yakan sami wani abin masarufi.
A taƙaice za a iya kasa kawalci zuwa manyan kaso guda uku
da suka haɗa da:
(1) Kawalcin Mata
Shi wannan nau’i na kawalci wasu mutane ne da suka ɗauki
wannan ɗabi’a a matsayin hanyar neman abin masarufi suke nama wa wasu mutane
mata suna kai musu da niyyar a aikata lalata, su kuma a biya su.
Suna gudanar da wannan ɗabi’a ne ta hanyar yarjejeniya ko
kuma yanke farashi. Ma’ana tun kafin su kawo wa mutum mace sai an ƙayyade abin
da za a biya su. Su waɗannan mutane suna nema wa mutum duk irin macen da yake
so, sannan kuma kowacce mace tana da farashi, ya danganta da ƙirarta.
(2) Kawalcin Maza
Nau’i na biyu wanda ya fi kowanne muni shi ne masu yin sa
sun mayar da hankali ne a kan nema wa mutane maza maimakon mata.
Su kawalan maza su ma mutane lalatattu, wasu ma suna
aikata irin wannan lalatar da maza, sukan yi haka ne ta hanyar yaudarar mutane
da wasu abubuwa. Sukan samu yara masu kwaɗayi su rinƙa ba su abubuwa na jin daɗin
rayuwa da yi musu alƙawari na cewa za su saya musu mota ko babur ko kuma su ce
za a kai su aikin Hajji idan suka amince aka aikata lalata da su.
Abin takaici a yanzu wannan ɗabi’a ta zama ruwan dare a
cikin al’ummar Hausawa da ma duniya bakiɗaya.
(3) Kawalcin Mata Da Maza
Wannan nau’i na kawalci ya fi sauran nau’o’in shahara da ɗaukaka.
Masu aikata wannan ɗabi’a sukan nemawa mata ko maza waɗanda za a yi aikin assha
da su.
Zaurancen Kawalai
Kawalai suna da zaurance na musamman da suke amfani da su
a lokacin da su a lokacin da suke aiwatar
da wannan ɗabi’ar. Misali a lokacin da suke zaune a majalisarsu ko
dandali duk mutumin da ya tunkaro su, idan suka ga ya yi kama da irin mutanen
da suke hulɗa da su, bayan sun gama gaisawa abu na farko da za su ce masa shi
ne.
“Alhaji me ake buƙata, kaza ko zakara?”
Shi kuwa idan abin da ya kawo shi kenan, sai ya zaɓa ya
ce; “Kaza” ko ya ce, “Zakara”
A zaurancen nasu abin da wai suke nufi da “kaza” shi ne “mace”
haka kuma abin da suke nufi da “zakara” shi ne “namiji.”
A mafi yawancin lokuta kawalai suna gane abokan harkar su
wato waɗanda za a nema a kai wa mutane ta hanyar wasu alamomi.
A ƙasashen da suka ci gaba kuwa sukan gane mata lalatattu
ta hanyar saka wata irin sarƙa a ƙafarsu ta hagu ko ta dama, ko kuma yin wani
ƙunshi na musamman a ƙafafuwansu ko kuma saka zobe a yatsan ƙafa.
Haka kuma sukan gane maza ta hanyar yin wani irin aski ko
kuma gyaran gashi na musamman. Ta haka ne su kawalan suna ganin su ko da kuwa
ba su taɓa ganin su ba, za su gane su, ta irin waɗannan alamomi.
Waɗannan alamomi sun yi nisa da zuwa ƙasar Hausa da
kewayenta.
Ba kowa ake yi wa kawalci ba, sai wasu keɓaɓɓun mutane waɗanda
ba sa so a gan su suna aikata irin wannan ɗabiu’ar. Snanan kuma yawanci shugabanni
ne a cikin al’umma, akan haka ne suke neman waɗanda za su riƙa yi musu kawalci,
suna biyan su.
Waɗansu daga cikin waɗanda ake yi wa kawalci akwai
attajirai da masu mulki da kuma wasu manyan mutane.
A mafi yawan lokaci kuwa su ne suke riƙe da ragamar
tafiyar da jagoranci na al’umma.
(A sani: Akwai wasu alamomi da alamtattuka da na ɓoye don
kar su zama abin koyi ga gurɓatattu)
Sunday, September 10, 2023
FASSARA A HARSHEN HAUSA
FASSARA A HARSHEN HAUSA
Kabiru Yusuf
MA’ANAR FASSARA
Fassara asalinta kalmar Larabci, wato aikatau. Ma’anar kalmar a Larabci, ita ce bayanin wani sashe na littafi ko juyar magana daga wani harshe (yare) zuwa wani; wato “tarjamatun”. A taƙaice tafinta ko bayyana ma’anar magana shi ake kira da Larabci “Tarjamah/Tafsir”. Tafsir kuwa, ainihin ma’anarta ita ce bayanin ayoyin Alƙur’ani. Saboda haka ma iya cewa Hausawa sun ari wannan kalma ta fassara ne daga “fassar” ko “Tafsir.”
Bisa wannan za mu iya bayyana man’anar fassara da cewa, hanya ce ta mai da wata magana ko salo ko zance na wani harshe (yare) zuwa wani harshe (yare) ba tare da an sami bambancin ma’ana ba.
Idan ana fassara, ana amfani da wasu ƙa’idoji ne don bayyana ma’ana mafi kusa ko dacewa daga harshe na farko da harshe na biyu ta fuskar ma’ana da salo a maganance, ko kuma a rubuce. Saboda haka, ashe ke nan fassara ba ta samuwa sai da harasa guda biyu (harshen zance) da kuma harshe na biyu (harshen fassara). Haka kuma mafassari dole ne ya kasance mai iya yaruka biyu zuwa sama. Wato, dole mafassari ya zama kanari ko coli wajen iya magana da harasa. Dalili shi ne, mai iya magana da harshe (yare) ɗya ba ya iya fassara, sai dai ya yi ƙarin bayani.
Misali, a cikin harshe guda, ana iya samun wata magana dunƙulalliyaa cikin salo na hikima kamar karin magana ko zaurance ko azanci, waɗanda suke buƙatar ƙarin bayani domin a fahince su.
Fassara tana da manyan rabe-rabe guda biyu waɗanda suka haɗa da; fassarar ilimi da fassarar adabi
1. Fassarar ilimi: ita ce wadda ta shafi kimiyya ko kuma addini. A nan duk abin da aka rubuta ta sha’anin ilimi, ƙoƙari za a yi a zuba mata ƙa’idoji ko a ba ka labarin wani abu kai tsaye kawai ba wani sanabe ko ado ko ƙaƙale. Wato dai a faɗi gundarin gaskiya abu yadda yake. Haka kuma, ana amfani da kalmomi tare da zaƙin murya na baliganci ko tsoratarwa ga abubuwan da suka shafi harkokin addinin domin jama’a su tsorata ko himmata wajen abin da ake son su yi ko su bari.
2. Fassarar adabi: ita wannan fassarar ta adabi kuwa, ita ce wadda ake so a faɗi wani abu da aka rubuta ko aka faɗa da salo na sanabe ko ƙaƙale, wani lokaci ma akan so a faɗi abu ɗaya da ma’anoni biyu ko fiye, yadda in an tashi takura mai faɗa ta nan sai ya ɓullo ta can ya ce, ai ga abin da yake nufi in an zo fassara irin wannan, dole ne a yi ƙoƙari a ƙaƙale da salo na kurɗa-kurɗa da za a iya, har ma inda dama a yi wa fassarar baki biyu in ana iyawa.
NAU’O’IN FASSARA
Babban abin da ake nema a fassara, shi ne fahintar abin da harshe na biyu ke magana kamar yadda ma’anarsa take a harshe na farko. Abin nufi a nan dole sai an fassara komai daidai sannan za a sami fahintar abu sosai. Saboda haka ashe ya zama wajibi mai fassara ya fahinci abin da yake fassarawa, don in bai fahinta ba, ba zai yiwu ya yi fassara ingantacciya yadda abin yake ba, wanda yin hakan shi ke sa ma’ana ta canza a kuma haddasa rashin fahinta ga masu karanta fassara ko saurare saboda ganin irin wannan ne a wani ra’ayi aka rarraba fassara zuwa kashi-kashi kamar haka:
(1) Fassarar Kalma Da Kalma/ Jimla Da Jimla
Ana yin fassarar kalma da kalma ko jimla da jimla kamar yadda yake a cikin harshen farko zuwa harshe na biyu ko da babu ma’ana.
Wani lokacin kuma ana ɗaukar kowanne sakin layi ne abin da ake so a fassara ba ta kalma da kalma ba, wato akan yi ne gwargwadon abin da sakin layi ya ƙunsa.
Misali: Good morning =Kyakkyawar safiya
A Hausa an ce: “Naira bibiyu ne kowanne”
“Two-two naira each”, maimakon “two naira each.”
Saboda haka irin wannan fassara a wani lokaci ba ta da daɗin karatu a wajen mai karantawa, kuma fahintar ma’anarta kan jirkita.
(2) Fassara Mai ‘Yanci
Fassara mai ‘yanci ita ce wadda za a yi bisa fahintar abin da aka karanta na cikin harshe na farko. Wato wannan fassarar, harshen da mai fassara ya karanta kuma ya fahinci abin da ake nufi, sai shi kuma ya rubuta cikin harshen da yake fassara mafi sauƙi yadda za a fahinta. Wato mai fassara na da ‘yancin faɗin abin da ya ga dama muddin dai ya bayar da ma’ana kamar yadda yake a harshe na farko.
Ita wannan fassara tana buƙatar lura ainun don gudun kada a yi ƙari ko ragi wanda bai dace ba a cikinta, kodayake dai ana iya taƙaita ta ko a tsawaita ta, amma dai fassara ce mai tara dukkan ma’anar abin da ake fassarawa.
(3) Fassarar Harshe Da Wani Harshe
Wato ita wannan fassarar, a wani lokaci akan sami mutum yana magana da wani harshe sannan kuma wani ya fassara maganar mutumin nan da wani harshe. Wannan irin fassarar na samu ne wajen magana a taro, inda wasu ba sa jin harshen wasu kamar yadda ake yi a majalisar ɗinkin duniya ko shugabannin ƙasashe ko kuma manyan jami’an diflomasiyya. Irin wannan fassara ita ake kira “Tafinta.”
MUHIMMANCIN FASSARA
(a) Ana fassara don kyautata danganatakar al’ummomi daban-daban
(b) Ana fassara littattafai don a haɓaka harkokin ilimi
(c) Ana fassara don wayar da kan al’umma
(d) Ana fassara don yaɗa manufofin gwamnati ko hukuma
(e) Ana fassara don haɓaka arziƙin ƙasa ta sanin wasu asiran ƙere-ƙere da hanyoyin kasuwanci
(f) Ba wa ɗan’adam damar laƙantar harasa da dama
ƘA’IDOJIN FASSARA
Akwai hanyoyi da ƙa’idoji da ya zama wajibi mai fassara ya bi su domin a fahinci saƙon da yake son isarwa ga jama’a. Waɗannan ƙa’idojin sun haɗa da:
(1) Mai fassara ya san manufar batu. Shin ya shafi kimiyya ne ko fasaha ko kuma kasuwanci?
(2) Mai fassara ya laƙanci harasan da zai yi fassara da su.
(3) Mai fassara ya san kalmomi da ma’anoninsu, musamman gama-garin kalmomi, irin su hannu, baki, ƙafasa, kai da sauransu.
(4) Sanin bambancin al’adu, domin harshe da al’adu Ɗanjuma ne da Ɗanjummai. Misali ƙanƙara da dusar ƙanƙara.
(5) Sanin kalmomi masu harshen damo, misali kamar a ce “jirgi” a nan jirgin na iya zama “jirgin sama” ko “na ruwa” ko na “ƙasa.” Da sauransu
(6) Mai fassara ya daidaita harshe, kuma ya san irin karin da zai yi amfani da shi domin a fahince shi da zarar ya ambaci kowacce irin kalma.
(7) La’akari da fifikon ma’ana a fassara wajibi ne, misali:
Good morning:
Kyakkyawar safiya Barka da asuba Ina kwana
(8) La’akari da mutanen da ake yi wa fassara shi ma wajibi ne. Ana so mafassari ya yi la’akari da basira da ilimi da shekaru na mutanen da yake yi wa fassara.
(9) Mai fassara ya yi fassara cikin daidaitacciyar Hausa ba cikin furucin Kananci ko Zazzaganci ko Katsinanci ko Dauranci ko Sakkwatanci ba. Haka kuma kada ya yi fassara cikin Ingausa.
(10) A yi la’akari da canza sigar jimloli domin su dace da harshen fassara. Kowane harshe da tsarin jimlolinsa. Misali a Hausa ana iya amfani da suna ko wakilin suna a jimla ɗaya, amma a Turanci haka ba ta faruwa. Misali: (a) Ado went to Kaduna. =Ado ya tafi Kaduna. (ba; Ado tafi Kaduna ba)
(b) He bought twelve cars. =Ya sayo motoci sha-biyu. (ba; Ya sayo sha-biyu motoci ba.)
(11) Ya zama mai bincike da neman cikakken bayanai game da ma’anar kalmomi tsofaffi da kuma sababbi.
(12) Mai fassara ya zama mai bin ƙa’idojin rubutu kamar yadda ƙa’idar harshe yake fassarata a ajiye. Misali: shi ne ba shine ba, ita ce ba itace ba, kowane ba ko wane ba, za a ba za’a ba da sauransu.
MATSALOLIN FASSARA A HARSHEN HAUSA
Harasa suna da hanyoyi da ba ƙayyadaddu ba, kuma rashin ƙayyadewa bisa abin da ya kamata a ce kaza a wannan harshe shi ne kaza a wancan harshen, shi ya kawo akasarin bambance-bambance a tsakanin harsuna. Taƙaitar wannan bambancin kuwa shi ne samuwar tsatso da asali da kuma cuɗanya tsakanin harasa.
Ire-iren wannan shi kan sa mutum ya iya yin kuskure, wato cewa ba ya yiwuwa a fassara zance daidai-wa-daida, wato ba ragi ba ƙari, haka kuma gwargwadon nisantar harasa gwargwadon salwatar manufa da ma’ana, amma duk da haka za a iya fassara zance ta hanyar tsantsar kalmomi ba damuwa da dangantakarsu ba.
Idan aka duba ‘yan shekarun baya, duk wanda ya liƙewa harshen Hausa, alhali ga ‘yan birni da ma’aikata tare da ‘yan makaranta kowa sai hanƙoro yake ya ji ana “yes, yes, no, no” to zai sha wuya, domin kuwa kallon biyu-ahu zai yi masa. Amma Allah da ikonsa, harshen Hausa ya sami wani matsayi na gogayya da wasu manyan harasa. Wannan shi ya sa ake ƙoƙarin gwada kalmominsa da nasu. Saboda haka wannan ya nuna ba wai a yanzu ne matsalar fassara ta fara ba, a’a tun lokacin da mutanen wata ƙasa suka fara kutso mana ne muka fara cin karo da waɗannan matsaloli:
1- Rashin Damuwa da kiyaye dangantakar da baƙuwar kalma take da ta Hausa;
2- Rashin sanin ita kanta baƙuwar kalma, balle a san ‘yar’uwarta a Hausa.
3- Rashin sanin kalmomin Hausa yadda za a ce ga ‘yan’uwansu a cikin baƙin kalmomi.
Waɗannan su suka sada arar wata kalma ta zo sai kawai mutane su bar harshen ya haɗiye ta don zafin da yake da shi, sai ka ga Hausar ta ainihi ta ɓace. A wannan magana da muke yi, akwai alamomi da yawa da muka ara waɗanda idan aka tsaya aka bincika za a iya gano ainihin takwarorinsu na Hausa domin kuwa akwai irin waɗannan kalmomi birjik a cikin adabin zamani, sai dai kula da rashin saninsu suka haddasa wannan. Wato, sai ka ga mutum wanda ya kamata ya fassara wata kalma, amma ƙuiya da rashin sani ya sa ya tsallake ta, kuma ya rafkana wajen fassarar ta, haka kuma za ta zauna har ‘ya’ya da jikoki.
Harshen Hausa ya fara cuɗanya da baƙin harasa. Cuɗanyar da ya yi a nan gida ita ce wadda ya yi da dukkan harsunan Najeriya. Amma waɗanda aka kawo tsaraba su ne Turanci da Larabci da kuma Faransanci da sauransu.
Saboda haka, idan har ana son gano yadda baƙuwar kalma kan shiga cikin wannan harshen na Hausa, dole ne a ɗauki wani baƙon harshe a yi amfani da shi. Alal misali; Larabci ya shigo ƙasar Hausa ta hanyoyi guda biyu, wato dalilin kasuwanci zuwa ƙasashen Larabawa kamar irin su Libiya, Sudan, Mali, Maroko da sauransu. Sannan kuma ta dalilin zuwan addinin Musulunci. Malamanmu na da, idan suna karatu sai su riƙa ƙyale wasu kalmomin Larabci suna tsunduma su cikin Hausa, maimakon su fassara su, amma saboda ƙuiya da rashin sani ya sa kalmomin ke yi wa harshen Hausa kane-kane, misali;
Larabci Hausa
Arziƙi maimakon wadata
Shagala maimakon mantuwa
Ilimi maimakon sani
Waɗannan kalmomi a koyaushe za ka ji malamai suna faɗarsu, kuma haka ake rubuta su. Haka abin yake faruwa da kalmomin Turanci waɗanda suka yi wa harshen Hausa kane-kane;
Turanci Hausa
Kwandem maimakon la’ana ko suka
Dameji maimakon lalacewa
Coci maimakon majami’a
Matsalar fili da lokaci ke haddasawa cikin jaridu. Abin nufi a nan shi ne, filin da za a sa Larabci da yawa kan jawo taƙaita fassara ko faɗaɗata. Matsalar lokaci kuwa ta shafi lokacin da aka ƙayyade wajen shirya jarida da lokacin da ake so a buga ta tafi don sayarwa ga jama’a.
Don haka ƙarancin lokaci da fili kan sa a yi wa labari yanka a yi aya a wurin da bai dace ba, ko kuma cire wani sashe da ba shi da muhimmanci.
SHAWARWARI GA MAI FASSARA CIKIN HARSHEN HAUSA
Duk mai fassara cikin harshen Hausa ta kowace irin hanyar sadarwa ga jama’a dole ne ya kasance ya yi la’akari da waɗannan shawarwari:
1. Dole ne ya kasance ya san harshen da yake so ya fassara da Hausa.
2. Dole ne ya san harshen Hausa, yadda zai iya gane kalmominta da kuma baƙin kalmomi.
Dangane da sigar Nahawu, kowace hanya aka bi sai an sami canji da ya shafi shigar Nahawu. Alal-misali; A Hausa za a iya haɗa suna da wakilin suna a cikin jimla guda, wanda Turanci bai yarda da wannan ba. Misali; Ado ya zo. Amma a Turanci sai dai “Ado come” ko “He came,” ba “Ado He came” ba.
Ta fuskar kalmomi da ma’anoninsu kuwa, ana la’akari da makusanciyarsu mafi dacewa, domin mutum zai haɗu da kalmomi gama-gari, misali; hannu, ƙafa, kai da sauransu da kuma kalmomi masu manufa ɗaya, amma suna da bambancin al’adu misali kamar “fari” da kuma “fat”. Sai kuma kalmomin da suke nuna zurfin ƙwarewa, misali;
Teargas =Barkonon tsohuwa
Senate =Majalisar Datijai
Salon zance da karin magana, kyawawan misalai ne da za mu iya amfani da su ta wajen irin juye-juyen da za mu iya yi wajen fassara. Idan mai fassara ya ci karo da salon ma’ana akwai abubuwa uku da zai iya yi;
(1) Salo zuwa salo
He is second to none;
Ba shi da na biyu.
(2) Juya ma’anar sarari zuwa salon zance.
Pride begets the turban of poverty;
=Girman kai rawanin tsiya
(3) Salon zance zuwa ma’ana sarari.
He was alarmed;
=Girmansa ya faɗi (ƙarin gishiri)
HANYOYIN MAGANCE MATSALOLIN FASSARA
Idan muka duba abubuwan da aka zayyana a baya dangane da matsalolin fassara, sai mu ga ita kanta matsalar fassara ba ta masu sadarwa ga jama’a ce kaɗai ba. Wannan matsala ce ta gwamnati wadda ya zama tilas a gare ta ta tashi tsaye wajen bai wa harsunan ƙasar nan wani matsayi da ya dace da su.
Hausawa sun ce, hannu ɗaya ba ya ɗaukar jinka. Saboda haka hanyoyin magance matsalolin fassara yanzu ta zama ta fassara da masu amfani da harshen.
(a) Masu fassara su san cewa fassara cikin harshen baka tana da fifiko kan fassara cikin rubutaccen zance.
(b) Masu fassara su san cewa maganar mutanen da ake yi wa fassara dangane da matsayinsu tana da fifiko kan fassara da ta fi yawan jama’a/mutane.
(c) Masu fassara su zama masu yawan gudanar da bincike akai-akai da kuma yawan halartar taron ƙarawa juna sani.
Manazarta
Tuntubi marubucin